< Zabura 69 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
Zborovođi. Po napjevu “Ljiljani”. Davidov. Spasi me, Bože: vode mi dođoše do grla!
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
U duboko blato zapadoh i nemam kamo nogu staviti; u duboku tonem vodu, pokrivaju me valovi.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
Iznemogoh od vikanja, grlo mi je promuklo, oči mi klonuše Boga mog čekajuć'.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Brojniji su od vlasi na glavi mojoj oni koji me mrze nizašto. Tvrđi su od kostiju mojih oni što mi se nepravedno protive: zar mogu vratiti što nisam oteo?
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
Bože, ti znadeš bezumnost moju, moji ti grijesi nisu sakriti.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Nek' se ne postide zbog mene koji se u te uzdaju, Gospode, Jahve nad Vojskama! Neka se ne posrame zbog mene koji traže tebe, Bože Izraelov!
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Jer zbog tebe podnesoh pogrdu, i stid mi pokri lice.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
Tuđinac postadoh braći i stranac djeci majke svoje.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Jer me izjela revnost za Dom tvoj i poruge onih koji se rugaju tebi padoše na me.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
Dušu sam postom mučio, okrenulo mi se u ruglo.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
Uzeh kostrijet za haljinu, i postah im igračka.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Koji sjede na vratima protiv mene govore, vinopije mi rugalice poju.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
No tebi se molim, Jahve, u vrijeme milosti, Bože; po velikoj dobroti svojoj ti me usliši po svojoj vjernoj pomoći!
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Izvuci me iz blata da ne potonem, od onih koji me mrze izbavi me - iz voda dubokih.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Nek' me ne pokriju valovi, nek' me ne proguta dubina, nek' bezdan ne zatvori usta nada mnom!
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Usliši me, Jahve, jer je dobrostiva milost tvoja, po velikom milosrđu pogledaj na me!
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Ne sakrivaj lica pred slugom svojim; jer sam u stisci, usliši me brzo!
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Približi se duši mojoj i spasi je; zbog dušmana mojih oslobodi me!
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Ti mi znadeš porugu, stid i sramotu, pred tvojim su očima svi koji me muče.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
Ruganje mi slomilo srce i klonuh; čekao sam da se tko sažali nada mnom, ali ga ne bi; i da me tko utješi, ali ga ne nađoh.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
U jelo mi žuči umiješaše, u mojoj me žeđi octom napojiše.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Nek' im stol bude zamka, a žrtvene gozbe stupica!
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Nek' im potamne oči da ne vide, nek' im bokovi zasvagda oslabe!
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Izlij na njih ljutinu, žar tvoga gnjeva nek' ih zahvati!
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Njihova kuća nek' opusti, u njihovu šatoru nek' nitko ne stanuje!
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
Jer su progonili koga ti pokara, bol povećaše onomu koga ti rani.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Na njihovu krivnju krivnju još dodaj, ne opravdali se pred tobom!
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Nek' budu izbrisani iz knjige živih, među pravednike neka se ne broje!
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
A ja sam jadnik i bolnik - nek' me štiti tvoja pomoć, o Bože!
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Božje ću ime hvaliti popijevkom, hvalit ću ga zahvalnicom.
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
Bit će to milije Jahvi no bik žrtveni, milije nego junac s papcima i rozima.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
Gledajte, ubogi, i radujte se, nek' vam oživi srce, svima koji Boga tražite.
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
Jer siromahe Jahve čuje, on ne prezire sužanja svojih.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Neka ga hvale nebesa i zemlja, mora i sve što se u njima miče.
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
Jer Bog će spasiti Sion - on će sagradit' gradove Judine - tu će oni stanovat', imati baštinu.
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
Baštinit će ga potomci slugu njegovih; prebivat će u njemu oni što ljube ime Božje.