< Zabura 69 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Da muryar “Lilin.” Ta Dawuda. Ka cece ni, ya Allah, gama ruwa ya kai wuyata
David kah Tuilipai te aka mawt ham Tui loh ka hinglu te ham pha dongah Pathen aw kai n'khang lah.
2 Na nutse cikin laka mai zurfi, inda babu wurin tsayawa. Na shiga cikin ruwaye masu zurfi; rigyawa ya sha kaina.
Sihnok laedil la ka buek tih tungtainah om kolla tui dung la ka pha voek dongah tuili loh kai n'yo coeng.
3 Na gaji da kira ina neman taimako; maƙogwarona ya bushe idanuna sun dushe, suna neman Allahna.
Ka pang te khaw ka kohnue coeng. Ka olrhong khaw koh coeng. Ka Pathen te ka lamtawn ah ka mik kha coeng.
4 Waɗanda suke ƙina ba dalili sun fi gashin kaina yawa; da yawa ne abokan gābana babu dalili, su da suke nema su hallaka ni. An tilasta mini in mayar da abin da ban sata ba.
Lunglilungl a la ka lunguet rhoek tah ka lu dongkah sam lakah yet. A honghi mai neh kai aka biit ka thunkha rhoek loh yet uh. Ka huen pawt te ka sah.
5 Ka san wautata, ya Allah; laifina ba a ɓoye yake daga gare ka ba.
Ka anglat te Pathen namah loh na ming tih ka dumlai he nang taeng lamloh a thuh uh moenih.
6 Bari waɗanda suke sa zuciya gare ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki; bari waɗanda suke neman ka kada su sha kunya saboda ni, Ya Allah na Isra’ila.
Ka Boeipa caempuei Yahovah, nang aka lamtawn rhoek te kai kong ah yahpok uh boel saeh. Israel Pathen nang aka tlap rhoek te kai kong ah a hmaithae uh boel saeh.
7 Gama na jimre da ba’a saboda kai, kunya kuma ta rufe fuskata.
Nang ham te kokhahnah ka phueih tih ka maelhmai he mingthae loh a dah.
8 Ni baƙo ne a cikin’yan’uwana, bare kuma ga’ya’yan mahaifiyata maza;
Ka pacaboeina rhoek taengah ka hlanglak tih ka manu ca rhoek taengah ka kholong.
9 gama himma da nake yi wa gidanka yana ƙunata, kuma zagi na masu zaginka yana fāɗuwa a kaina.
Na im thatlainah dongah kai n'yoop tih nang aka veet rhoek kah kokhahnah khaw kai soah tla.
10 Sa’ad da na yi kuka na kuma yi azumi dole in jimre da ba’a;
Te dongah ka hinglu kah yaehnah neh ka rhap dae kai taengah kokhahnah la pawk.
11 sa’ad da na sanya rigunan makoki, mutane suna maishe ni abin dariya.
Ka tlamhni pueinak ka bai vaengah amih ham thuidoeknah la ka om.
12 Masu zama a ƙofa suna mini ba’a, na zama waƙa a bakin bugaggu da giya.
Vong ka kah aka ngol rhoek loh kai taengah lolmang a taeng uh tih yu o rhoek kah rhotoeng la ka om khoeng.
13 Amma na yi addu’a gare ka, ya Ubangiji, a lokacin da ka ga dama; a cikin ƙaunarka mai girma, ya Allah, ka amsa mini da tabbacin ceto.
Tedae Pathen kah kolonah tue vaengah, kai loh BOEIPA nang taengah ka thangthuinah te, na sitlohnah cangpai dongah namah kah khangnah oltak neh kai nan doo.
14 Ka fid da ni daga laka, kada ka bari in nutse; ka cece ni daga waɗanda suke ƙina, daga rurin ruwaye.
Tangnong khui lamkah kai n'huul lamtah m'buek sak boeh. Ka lunguet neh tui dung lamkah n'huul lah.
15 Kada ka bar rigyawa yă sha kaina ko zurfafa su haɗiye ni ko rami yă rufe bakinsa a kaina.
Tuili tui loh kai n'yo boel saeh lamtah a laedil la kai n'yoop boel saeh. Tangrhom loh kai a ka n'khuep thil boel saeh.
16 Ka amsa mini, ya Ubangiji cikin alherin ƙaunarka; cikin jinƙanka mai girma ka juyo gare ni.
Na sitlohnah a then dongah kai n'doo lah BOEIPA. Na haidamnah cungkuem neh kai taengla ha mael lah.
17 Kada ka ɓoye fuskarka daga bawanka; ka amsa mini da sauri, gama ina cikin wahala.
Te dongah na maelhmai te na sal taeng lamkah thuh boel mai. Ka taengah n'daengdaeh dongah a loe la kai n'doo dae.
18 Ka zo kusa ka kuɓutar da ni; ka fanshe ni saboda maƙiyana.
Ka hinglu taengla ha yoei lamtah n'tlan dae. Ka thunkha rhoek kongah kai n'lat dae.
19 Ka san yadda ake mini ba’a, ake kunyatar da ni da kuma yadda nake shan kunya; dukan abokan gābana suna a gabanka.
Namah loh kai kah kokhahnah, yahpohnah, ka mingthae neh na hmaikah kai aka daengdaeh boeih khaw na ming.
20 Ba’a ta sa zuciyata ta karai ta bar ni ba mataimaki; Na nemi a ji tausayina, amma ban sami ko ɗaya ba, na nemi masu ta’aziyya, amma ban sami ko ɗaya ba.
Kokhahnah dongah ka lungbuei rhek tih ka mangoeng sut. Te dongah aka suem ham ka lamtawn dae om pawt tih, aka hloep ham khaw ka hmu pawh.
21 Sun sa abin ɗaci cikin abincina suka kuma ba ni ruwan inabi mai tsami sa’ad da nake jin ƙishi.
Ka buh dongah anrhat han hlum uh tih ka tuihalh vaengkah ham a thuui n'tul uh.
22 Bari teburin da aka shirya a gabansu yă zama musu tarko; bari yă zama sakamakon laifi da kuma tarko.
Amih kah caboei te amih mikhmuh ah pael la, rhoepnah te hlaeh la om pah saeh.
23 Bari idanunsu yă dushe don kada su gani, bayansu kuma yă tanƙware har abada.
Amih kah mik te a tueng khui lamkah hmuep saeh lamtah a cinghen khaw khun yoeyah saeh.
24 Ka kwarara fushinka a kansu; bari fushinka mai zafi yă ci musu.
Amih te na kosi lun thil lamtah na thintoek thinsa loh amih te doom saeh.
25 Bari wurinsu yă zama kufai; kada ka bar wani yă zauna a tentunansu.
Amih kah lumim te kho pong la om saeh lamtah a dap ah khosa hlang om boel saeh.
26 Gama sun tsananta wa waɗanda ka hukunta suna kuma taɗin wahalar waɗanda ka ji musu rauni.
Na ngawn te a hloem uh tih na rhok kah nganboh te a tae uh.
27 Ka neme su da laifi a kan laifi; kada ka bar su su sami rabo a cikin cetonka.
Thaesainah te amamih kathaesainah neh a koei dongah nang kah duengnah te bawn uh boel saeh.
28 Bari a shafe su sarai daga littafin rai kada a kuma lissafta su tare da adalai.
Hingnah cabu khui lamkah phae lamtah hlang dueng rhoek neh hmaih daek boeh.
29 Ina cikin zafi da kuma azaba; bari cetonka, ya Allah, yă tsare ni.
Tedae kai mangdaeng thakkhoeih he, Pathen namah kah khangnah neh n'hoeptlang lah.
30 Zan yabe sunan Allah cikin waƙa in kuma ɗaukaka shi tare wurin yin godiya.
Lumla a neh Pathen ming te ka thangthen vetih amah te uemonah neh ka pomsang puei ni.
31 Wannan zai gamshi Ubangiji fiye da saniya, fiye da bijimi da ƙahoninsa da kuma kofatansa.
Te daengah ni BOEIPA ham vaito vaitotal ki cawn neh khomae aka rhak lakah a uemo eh.
32 Matalauta za su gani su kuma yi murna, ku da kuke neman Allah, bari zukatanku su rayu!
Kodo rhoek loh a hmuh vetih a kohoe uh ni. Pathen aka tlap rhoek, nangmih thinko ah hing van saeh.
33 Ubangiji yakan ji masu bukata ba ya kuwa ƙyale kamammun mutanensa.
BOEIPA loh khodaeng rhoek te a yaak tih a thongtla rhoek khaw a hnoel moenih.
34 Bari sama da ƙasa su yabe shi, tekuna da dukan abin da yake motsi a cikinsu,
Vaan rhoek neh diklai loh, tuitunli rhoek neh a khuiah aka yuel boeih loh BOEIPA amah te thangthen uh saeh.
35 gama Allah zai cece Sihiyona yă sāke gina biranen Yahuda. Sa’an nan mutane za su zauna a can su mallake ta,
Pathen loh Zion a khang ni. Judah khopuei rhoek te a sak vaengah kho a sak vetih pahoi a pang uh ni.
36 ’ya’yan bayinsa za su gāje ta, waɗanda kuma suna ƙaunar sunansa za su zauna a can.
A sal rhoek kah a tiingan long khaw a pang uh vetih a ming aka lungnah rhoek loh a khuiah kho a sakuh.

< Zabura 69 >