< Zabura 68 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
För sångmästaren; av David; en psalm, en sång.
2 Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
Gud står upp; hans fiender varda förskingrade, och de som hata honom fly för hans ansikte.
3 Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
Såsom rök fördrives, så fördrivas de av dig; likasom vaxet smälter för eld, så förgås de ogudaktiga för Guds ansikte.
4 Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
Men de rättfärdiga äro glada, de fröjda sig inför Gud och jubla i glädje.
5 Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
Sjungen till Guds ära, lovsägen hans namn. Gören väg för honom som drager fram genom öknarna. Hans namn är HERREN, fröjdens inför honom;
6 Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
de faderlösas fader och änkors försvarare, Gud i sin heliga boning,
7 Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
en Gud som förhjälper de ensamma till ett hem, och som för de fångna ut till lycka; allenast de gensträviga måste bo i en öken.
8 duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
Gud, när du drog ut i spetsen för ditt folk, när du gick fram i ödemarken, (Sela)
9 Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
då bävade jorden, då utgöt himmelen sina flöden inför Guds ansikte; ja, Sinai bävade för Guds ansikte; Israels Guds.
10 Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
Ett nåderikt regn lät du falla, o Gud; ditt arvland, som försmäktade, vederkvickte du.
11 Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
Din skara fick bo däri; genom din godhet beredde du det åt de betryckta, o Gud.
12 “Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
Herren låter höra sitt ord, stor är skaran av kvinnor som båda glädje:
13 Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
»Härskarornas konungar fly, de fly, och husmodern därhemma får utskifta byte.
14 Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
Viljen I då ligga stilla inom edra hägnader? Duvans vingar äro höljda i silver, och hennes fjädrar skimra av guld.
15 Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
När den Allsmäktige förströr konungarna i landet, faller snö på Salmon.»
16 Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
Ett Guds berg är Basans berg, ett högtoppigt berg är Basans berg.
17 Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
Men varför sen I så avogt, I höga berg, på det berg som Gud har utkorat till sitt säte, det där ock HERREN skall bo för alltid?
18 Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
Guds vagnar äro tiotusenden, tusen och åter tusen; Herren drog fram med dem, Sinai är nu i helgedomen.
19 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
Du for upp i höjden, du tog fångar, du undfick gåvor bland människorna, ja, också de gensträviga skola bo hos HERREN Gud.
20 Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
Lovad vare Herren! Dag efter dag bär han oss; Gud är vår frälsning. (Sela)
21 Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
Gud är för oss en Gud som frälsar, och hos HERREN, Herren finnes räddning från döden.
22 Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
Men Gud sönderkrossar sina fienders huvuden, krossar hjässan på den som går där med skuld.
23 don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
Herren säger: »Från Basan skall jag hämta dem, från havets djup skall jag hämta dem upp,
24 Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
så att du kan stampa med din fot i blod och låta dina hundars tunga få sin del av fienderna.»
25 A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
Man ser, o Gud, ditt högtidståg, min Guds, min konungs, tåg inne i helgedomen.
26 Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
Främst gå sångare, harpospelare följa efter, mitt ibland unga kvinnor som slå på pukor.
27 Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
Lova Gud i församlingarna, loven Herren, I av Israels brunn.
28 Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
Där går Benjamin, den yngste, han för dem an; där går skaran av Juda furstar, Sebulons furstar, Naftalis furstar.
29 Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
Din Gud har beskärt dig makt; så håll nu vid makt, o Gud, vad du har gjort för oss.
30 Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
I ditt tempel i Jerusalem bäre konungar fram sina skänker åt dig.
31 Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
Näps odjuret i vassen, tjurarnas hop med deras kalvar, folken, må de ödmjukt hylla dig med sina silverstycken. Ja, han förströr de folk som finna behag i krig.
32 Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
De mäktige skola komma hit från Egypten, Etiopien skall skynda hit till Gud, med gåvor i händerna.
33 gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
I riken på jorden, sjungen till Guds ära; lovsägen Herren, (Sela)
34 Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
honom som far fram på urtidshimlarnas himmel. Ja, där låter han höra sin röst, en mäktig röst.
35 Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!
Given Gud makten; över Israel är hans härlighet, och hans makt är i skyarna. Fruktansvärd är du, Gud, i din helgedom; Israels Gud, han giver makt och styrka åt sitt folk. Lovad vare Gud!

< Zabura 68 >