< Zabura 68 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
Til sangmesteren; av David; en salme, en sang. Gud reiser sig, hans fiender spredes, og de som hater ham, flyr for hans åsyn.
2 Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
Likesom røk drives bort, så driver du dem bort; likesom voks smelter for ild, forgår de ugudelige for Guds åsyn.
3 Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
Og de rettferdige gleder sig, de jubler for Guds åsyn og fryder sig med glede.
4 Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
Syng for Gud, lovsyng hans navn, gjør vei for ham som farer frem på de øde marker, Herren er hans navn, og juble for hans åsyn!
5 Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
Farløses far og enkers dommer er Gud i sin hellige bolig.
6 Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
Gud gir de enslige hus, fører fanger ut til lykke; bare de gjenstridige bor i et tørt land.
7 Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
Gud, da du drog ut foran ditt folk, da du skred frem gjennem ørkenen, (sela)
8 duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
da bevet jorden, og himlene dryppet for Guds åsyn, Sinai der borte, for Guds, Israels Guds åsyn.
9 Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
Et rikelig regn spredte du, Gud; din arv, den utmattede, styrket du.
10 Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
Ditt folk bosatte sig i landet; du laget det ved din godhet i stand for den elendige, Gud!
11 Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
Herren gir seierssang; stor er skaren av kvinner med gledesbudskap.
12 “Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
Hærenes konger flyr, de flyr, og hun som sitter hjemme, deler bytte.
13 Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
Når I hviler mellem kveene, er det som en dues vinger, som er dekket med sølv, og hvis vingefjær har gullets grønnlige glans.
14 Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
Når den Allmektige spreder konger der, da sner det på Salmon.
15 Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
Et Guds fjell er Basans fjell, et fjell med mange tinder er Basans fjell.
16 Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
Hvorfor ser I skjevt, I fjell med de mange tinder, til det fjell som Gud finner behag i å bo på? Herren skal også bo der evindelig.
17 Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
Guds vogner er to ganger ti tusen, tusen og atter tusen; Herren er iblandt dem, Sinai er i helligdommen.
18 Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
Du fór op i det høie, bortførte fanger, tok gaver blandt menneskene, også blandt de gjenstridige, for å bo der, Herre Gud!
19 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
Lovet være Herren dag efter dag! Legger man byrde på oss, så er Gud vår frelser. (Sela)
20 Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
Gud er oss en Gud til frelse, og hos Herren, Israels Gud, er det utganger fra døden.
21 Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
Ja, Gud knuser sine fienders hode, den hårrike isse på ham som vandrer i sin syndeskyld.
22 Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
Herren sier: Fra Basan vil jeg hente tilbake, jeg vil hente tilbake fra havets dyp,
23 don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
forat din fot må stampe i blod, dine hunders tunge få sin del av fiendene.
24 Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
De ser dine seierstog, Gud, min Guds, min konges, seierstog inn i helligdommen.
25 A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
Foran går sangere, bakefter harpespillere midt imellem jomfruer som slår på pauke.
26 Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
Lov Gud i forsamlingene, lov Herren, I som er av Israels kilde!
27 Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
Der er Benjamin, den yngste, som hersker over dem, Judas fyrster med sin skare, Sebulons fyrster, Naftalis fyrster.
28 Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
Din Gud har tildelt dig styrke; styrk, Gud, det du har gjort for oss!
29 Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
For ditt tempel i Jerusalems skyld skal konger komme til dig med gaver.
30 Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
Skjell på dyret i sivet, på stuteflokken med folke-kalvene, som kaster sig ned for dig med sølvstykker! Han spreder folkene som har lyst til strid.
31 Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
Veldige menn skal komme fra Egypten, Etiopia skal i hast utrekke sine hender til Gud.
32 Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
I jordens riker, syng for Gud, lovsyng Herren, (sela)
33 gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
ham som farer frem i himlenes himler, de eldgamle! Se, han lar sin røst høre, en mektig røst.
34 Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
Gi Gud makt! Over Israel er hans høihet, og hans makt i skyene.
35 Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!
Forferdelig er du, Gud, fra dine helligdommer; Israels Gud, han gir folket makt og styrke. Lovet være Gud!

< Zabura 68 >