< Zabura 68 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
UNkulunkulu kavuke, zihlakazeke izitha zakhe, labamzondayo babaleke phambi kwakhe.
2 Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
Njengokuphetshethwa kwentuthu baphephethe; njengokuncibilikiswa kwengcino phambi komlilo, ababi kabachithwe phambi kukaNkulunkulu.
3 Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
Kodwa abalungileyo kabajabule, bathabe phambi kukaNkulunkulu, njalo bathokoze ngentokozo.
4 Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
Hlabelelani kuNkulunkulu, hlabelelani indumiso ebizweni lakhe, limphakamise lowo ogade esedlula emagcekeni enkangala ngebizo lakhe uJehova, njalo thokozani phambi kwakhe.
5 Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
Unguyise wezintandane lomahluleli wabafelokazi, uNkulunkulu endaweni yakhe yokuhlala engcwele.
6 Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
UNkulunkulu uhlalisa ababodwa emulini, ukhupha ababotshiweyo ebasa empumelelweni, kodwa abalenkani bahlala elizweni elomileyo.
7 Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
Nkulunkulu, ekuphumeni kwakho phambi kwabantu bakho, ekuhambeni kwakho enkangala; (Sela)
8 duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
Umhlaba wazamazama, lawo amazulu athontisa phambi kukaNkulunkulu, le iSinayi, phambi kukaNkulunkulu, uNkulunkulu kaIsrayeli.
9 Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
Walinisa izulu elikhulu, Nkulunkulu; waliqinisa wena ilifa lakho selikhathele.
10 Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
Ibandla lakho lahlala kulo; wamlungisela ngobuhle bakho oswelayo, Nkulunkulu.
11 Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
INkosi yanika ilizwi; abesifazana ababika izindaba babelixuku elikhulu.
12 “Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
Amakhosi amabutho ayabaleka, ayabaleka. Owesifazana ohlezi ekhaya wayaba impango.
13 Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
Lanxa lilala phakathi kwezibaya zezimvu, lizakuba njengempiko zejuba ezisitshekelwe ngesiliva, lezinsiba zalo ngegolide eliliganu.
14 Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
Lapho uSomandla echitha amakhosi kulo, kwaba mhlophe njengeliqhwa elikhithikileyo eZalimoni.
15 Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
Intaba yeBashani yintaba kaNkulunkulu, intaba elezingqonga, intaba yeBashani.
16 Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
Likhangelelani ngomhawu, lina zintaba zezingqonga? Lintaba uNkulunkulu uyiloyisele ukuhlala kwakhe. Yebo, iNkosi izahlala kuyo kuze kube nininini.
17 Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
Izinqola zikaNkulunkulu ziyizinkulungwane ezingamatshumi amabili, izinkulungwane zezinkulungwane, iNkosi iphakathi kwazo, iSinayi endaweni engcwele.
18 Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
Wena wenyukele phezulu, wathumba abathunjiweyo; wemukela izipho ebantwini, yebo, lakwabalenkani; ukuze uJehova uNkulunkulu ahlale khona.
19 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
Kayibongwe iNkosi; isethwesa insuku ngensuku; uNkulunkulu ulusindiso lwethu. (Sela)
20 Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
UNkulunkulu wethu unguNkulunkulu wezinsindiso; lakuJehova iNkosi kulokuphuma ekufeni.
21 Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
Kodwa uNkulunkulu uzaphohloza ikhanda lezitha zakhe, ukhakhayi olulenwele lwalowo ohamba ezonweni zakhe.
22 Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
INkosi yathi: Ngizababuyisa bevela eBashani, ngibabuyise bevela enzikini yolwandle,
23 don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
ukuze inyawo zakho uzigxamuze egazini lezitha, inlimi zezinja zakho kulo.
24 Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
Zibonile izindwendwe zakho, Nkulunkulu; izindwendwe zikaNkulunkulu wami, iNkosi yami, endaweni engcwele.
25 A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
Ngaphambili kuhamba abahlabelayo, ngemuva abatshayi bamachacho, phakathi izintombi zitshaya izigubhu.
26 Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
Bongani uNkulunkulu emabandleni, iNkosi, kuvela emthonjeni kaIsrayeli.
27 Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
Nango uBhenjamini omncinyane umbusi wabo, iziphathamandla zikaJuda, inkundla yazo, iziphathamandla zikaZebuluni, iziphathamandla zikaNafithali.
28 Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
UNkulunkulu wakho ulaye amandla akho; qinisa, Nkulunkulu, lokho osenzele khona.
29 Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
Ngenxa yethempeli lakho eJerusalema amakhosi azakulethela isipho.
30 Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
Sikhuze isilo somhlanga, umhlambi wezinkunzi kanye lamankonyana abantu, kuze kuthobeke kulenhlamvu zesiliva; ubahlakaze abantu abathokoza ezimpini.
31 Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
Iziphathamandla zizakuza zivela eGibhithe; iEthiyophiya izakwelulela izandla zayo kuNkulunkulu ngokuphangisa.
32 Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
Mibuso yomhlaba, hlabelelani kuNkulunkulu, lihlabelele indumiso eNkosini. (Sela)
33 gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
Kuyo egade phezu kwamazulu amazulu awendulo; khangelani, iphumisa ilizwi layo, ilizwi elilamandla.
34 Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
Phanini amandla kuNkulunkulu; ubukhosi bakhe buphezu kukaIsrayeli, lamandla akhe asemayezini.
35 Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!
Uyesabeka, Nkulunkulu, ezindaweni zakho ezingcwele; uNkulunkulu kaIsrayeli nguye onika abantu bakhe amandla lengalo. Kabongwe uNkulunkulu.

< Zabura 68 >