< Zabura 68 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
Au maître chantre. Cantique de David. Que Dieu se lève, ses ennemis se dissipent, et ses adversaires fuient sa présence.
2 Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
Tu les balaies, comme une fumée chassée; de même que la cire fond au feu, ainsi disparaissent les impies devant Dieu.
3 Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
Et les justes sont transportés, ravis devant Dieu, et tressaillent d'allégresse.
4 Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
Chantez Dieu, célébrez son nom! Ouvrez-lui les chemins, Il s'avance au désert! L'Éternel est son nom; réjouissez-vous à son aspect!
5 Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
Père des orphelins et défenseur des veuves, tel est notre Dieu dans sa demeure sainte;
6 Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
Il donne aux bannis une habitation, Il élargit les captifs pour les rendre heureux; seuls les rebelles habitent une terre aride.
7 Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
O Dieu, quand tu sortis à la tête de ton peuple, quand tu t'avançais traversant le désert, (Pause)
8 duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
la terre trembla, et les Cieux ruisselèrent en présence de Dieu; ce Sinaï trembla devant Dieu, le Dieu d'Israël.
9 Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
Tu fis tomber, ô Dieu, une rosée bienfaisante, et tu restauras ton héritage épuisé.
10 Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
Ton peuple s'établit en ce lieu; tu l'avais, ô Dieu, préparé dans ta bonté pour les malheureux!
11 Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
Dieu fit entendre les hymnes des femmes annonçant la victoire à la grande armée:
12 “Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
« Les rois des nations fuient, ils fuient, et celle qui garde le logis, distribue le butin.
13 Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
Tandis que vous goûtez le repos parmi les bergeries, vous recevez des ailes de colombes recouvertes d'argent et leur plumage orné de l'or pâle. »
14 Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
Lorsque dans ce lieu le Tout-puissant dispersa les rois, le sol blanchit, comme le Salmon, quand il neige.
15 Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
Montagnes de Dieu, monts de Basan, monts aux cimes nombreuses, monts de Basan,
16 Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
pourquoi, cimes et montagnes, ces regards d'envie contre la montagne que Dieu choisit pour sa demeure? Aussi bien Il l'habite pour jamais!
17 Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
Les chars de Dieu sont deux fois dix mille, des milliers, et encore des milliers; le Seigneur est au milieu; Sinaï est dans le Sanctuaire!
18 Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
Tu montes sur la hauteur, tu mènes des captifs; tu reçois des hommes en don; les rebelles aussi viennent habiter avec l'Éternel Dieu.
19 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
Que le Seigneur soit béni chaque jour! Nous charge-t-on d'un fardeau, Dieu est notre aide. (Pause)
20 Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
Ce Dieu est pour nous un Dieu secourable, et l'Éternel, le Seigneur, sait nous soustraire à la mort.
21 Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
Oui, Dieu frappera la tête de ses ennemis, le crâne chevelu de ceux qui suivent la voie de leur crime.
22 Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
Le Seigneur dit: « Je les ramènerai de Basan, les ramènerai du fond de la mer;
23 don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
afin que tu remues tes pieds dans le sang, et que la langue des chiens ait part au sang de tes ennemis. »
24 Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
Ils contemplent ta marche, ô Dieu, la marche de mon Dieu, de mon Roi dans le Sanctuaire.
25 A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
En tête sont les chantres, après eux les musiciens, au milieu des vierges qui agitent les cymbales.
26 Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
« En chœur bénissez Dieu, le Seigneur, vous qui sortez de la source d'Israël! »
27 Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
Là est Benjamin le jeune, et ses chefs, les princes de Juda, et sa multitude, les princes de Zabulon, les princes de Nephthali.
28 Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
[Israël!] ton Dieu a décrété ta puissance: montre-toi puissant, ô Dieu, qui as agi pour nous,
29 Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
de ton temple qui domine Jérusalem! Que les rois t'apportent leurs offrandes!
30 Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
Gourmande le monstre qui gîte dans les roseaux, la troupe des taureaux escortés des veaux des nations! Les faisant venir à Ses pieds avec des pièces d'argent, Il dissipe les peuples qui se plaisent aux combats.
31 Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
Des Grands arrivent de l'Egypte, et l'Ethiopie accourt, les mains tendues vers Dieu.
32 Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
Royaumes de la terre, élevez à Dieu vos cantiques, par vos concerts célébrez le Seigneur, (Pause)
33 gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
qui s'avance dans les espaces des Cieux éternels: voici, de sa voix Il produit des éclats puissants.
34 Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
Rendez l'honneur à Dieu, dont la majesté protège Israël, et dont la puissance apparaît dans les nues!
35 Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!
De ton Sanctuaire, ô Dieu, tu es redoutable. C'est le Dieu d'Israël, qui donne force et puissance à son peuple. Béni soit Dieu!

< Zabura 68 >