< Zabura 68 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
Psaume de Cantique, de David, [donné] au maître chantre. Que Dieu se lève, et ses ennemis seront dispersés, et ceux qui le haïssent s'enfuiront de devant lui.
2 Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
Tu les chasseras comme la fumée est chassée [par le vent]; comme la cire se fond devant le feu, [ainsi] les méchants périront devant Dieu.
3 Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
Mais les justes se réjouiront et s'égayeront devant Dieu, et tressailliront de joie.
4 Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
Chantez à Dieu, psalmodiez son Nom, exaltez celui qui est monté sur les cieux; son Nom, est l'Eternel; et égayez-vous en sa présence.
5 Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
Il est le père des orphelins, et le juge des veuves; Dieu est dans la demeure de sa Sainteté.
6 Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
Dieu fait habiter en famille ceux qui étaient seuls; il délivre ceux qui étaient enchaînés, mais les revêches demeurent en une terre déserte.
7 Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
Ô Dieu! Quand tu sortis devant ton peuple, quand tu marchais par le désert; (Sélah)
8 duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
La terre trembla, et les cieux répandirent leurs eaux à cause de la présence de Dieu, ce mont de Sinaï [trembla] à cause de la présence de Dieu, du Dieu d'Israël.
9 Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
Ô Dieu! tu as fait tomber une pluie abondante sur ton héritage; et quand il était las, tu l'as rétabli.
10 Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
Ton troupeau s'y est tenu. Tu accommodes de tes biens celui qui est affligé, ô Dieu!
11 Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
Le Seigneur a donné de quoi parler; les messagers de bonnes nouvelles ont été une grande armée.
12 “Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
Les Rois des armées s'en sont fuis, ils s'en sont fuis, et celle qui se tenait à la maison a partagé le butin.
13 Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
Quand vous auriez couché entre les chenets arrangés, [vous serez comme] les ailes d'un pigeon couvert d'argent, et dont les ailes sont [comme] la couleur jaune du fin or.
14 Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
Quand le Tout-puissant dissipa les Rois en cet [héritage], il devint blanc, comme la neige qui est en Tsalmon.
15 Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
La montagne de Dieu est un mont de Basan; une montagne élevée, un mont de Basan.
16 Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
Pourquoi lui insultez-vous, montagnes dont le sommet est élevé? Dieu a désiré cette montagne pour y habiter, et l'Eternel y demeurera à jamais.
17 Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
La chevalerie de Dieu [se compte par] vingt-mille, par des milliers redoublés; le Seigneur est au milieu d'eux; c'est un Sinaï en Sainteté.
18 Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
Tu es monté en haut, tu as mené captifs les prisonniers, tu as pris des dons [pour les distribuer] entre les hommes, et même entre les rebelles, afin qu'ils habitent [dans le lieu] de l'Eternel Dieu.
19 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
Béni soit le Seigneur, qui tous les jours nous comble de ses biens; le [Dieu] Fort est notre délivrance; (Sélah)
20 Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
Le [Dieu] Fort nous est un [Dieu] Fort pour nous délivrer, et les issues de la mort sont à l'Eternel le Seigneur.
21 Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
Certainement Dieu écrasera la tête de ses ennemis, le sommet de la tête chevelue de celui qui marche dans ses vices.
22 Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
Le Seigneur a dit: je ferai retourner [les miens] de Basan, je les ferai retourner du fond de la mer.
23 don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
Afin que ton pied et la langue de tes chiens s'enfoncent dans le sang des ennemis, [dans le sang] de chacun d'eux.
24 Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
Ô Dieu! Ils ont vu tes démarches dans le lieu saint, les démarches de mon [Dieu] Fort, mon Roi.
25 A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
Les chantres allaient devant, ensuite les joueurs d'instruments, [et] au milieu les jeunes filles, jouant du tambour.
26 Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
Bénissez Dieu dans les assemblées, [bénissez] le Seigneur, vous qui êtes de la source d'Israël.
27 Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
Là Benjamin le petit a dominé sur eux; les principaux de Juda ont été leur accablement de pierres: [là ont dominé] les principaux de Zabulon, [et] les principaux de Nephthali.
28 Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
Ton Dieu a ordonné ta force. Donne force, ô Dieu; c'est toi qui nous as fait ceci.
29 Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
Dans ton Temple, à Jérusalem, les Rois t'amèneront des présents.
30 Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
Tance rudement les bêtes sauvages des roseaux, l'assemblée des forts taureaux, et les veaux des peuples, [et] ceux qui se montrent parés de lames d'argent. Il a dissipé les peuples qui ne demandent que la guerre.
31 Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
De grands Seigneurs viendront d'Egypte; Cus se hâtera d'étendre ses mains vers Dieu.
32 Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
Royaumes de la terre, chantez à Dieu, psalmodiez au Seigneur; (Sélah)
33 gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
[Psalmodiez] à celui qui est monté dans les cieux des cieux qui sont d'ancienneté; voilà, il fait retentir de sa voix un son véhément.
34 Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
Attribuez la force à Dieu; sa magnificence est sur Israël, et sa force est dans les nuées.
35 Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!
Ô Dieu! Tu es redouté à cause de tes Sanctuaires. Le [Dieu] Fort d'Israël est celui qui donne la force et la puissance à son peuple; Béni soit Dieu!

< Zabura 68 >