< Zabura 68 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
God, arise and scatter your enemies, and cause those who hate you to run away from you.
2 Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
Like [wind] blows smoke away, chase your enemies away. Like wax melts when it is near a fire, cause wicked people to (disappear/be destroyed).
3 Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
But righteous people should be joyful; they should rejoice when they are in God’s presence; they should be happy, and be very joyful.
4 Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
Sing to God; sing to praise him; sing a song (OR, make a road) for him who rides on the clouds; his name is Yahweh; be glad when you are in his presence.
5 Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
God, who lives in his sacred temple, is [like] [MET] a father to [those who are] orphans, and he is the one who protects widows.
6 Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
For those who have no one to live with, he provides families [to live with]. He frees prisoners and enables them to be successful, but those who rebel [against him] will be forced to live in a very hot and dry land.
7 Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
God, you led your people out [of Egypt], and then you marched with them through the desert.
8 duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
After you did that, because when you, the God [worshiped by us] Israeli people, appeared to us at Sinai [Mountain], the earth shook, and rain poured down from the sky.
9 Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
You caused plenty of rain to fall [on your land], [and so] you enabled good crops to grow again on the land that you gave [to us Israelis].
10 Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
Your people built homes there; and because you were good to them, you provided [food] for those who were poor.
11 Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
The Lord gave a message, and many women took that message to other places.
12 “Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
[They proclaimed], “Many kings and their armies are running away [from our army]!” [When our army brought back to their homes] the things that they captured, the women who were at home divided up those things [among themselves and among their families].
13 Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
Even those women who were in the pens [taking care of] the sheep [received some of those things]; they got statues of doves whose wings were covered with silver and whose feathers were covered with pure yellow gold.
14 Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
When Almighty [God] scattered the [enemy] kings [and their armies], [the number of weapons that they abandoned there] seemed like there had been a snowstorm on Zalmon (OR, a black) [Mountain].
15 Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
There is a very high mountain in the Bashan [region], a mountain which has many peaks.
16 Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
But the [people who live near] that mountain should not [RHQ] envy those who live near [Zion], the mountain on which God chose to live! Yahweh will live there forever!
17 Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
[After we defeated all our enemies], [it was as though] the Lord, surrounded by many thousands of strong chariots, descended from Sinai [Mountain] and came into the sacred temple [in Jerusalem].
18 Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
He ascended the sacred mountain [where his temple is], and took with him many people who had been captured [in battles]; and received gifts from the enemies [whom he had defeated]. He received gifts even from those who had rebelled against him, and Yahweh our God will live there [in his sacred temple] forever.
19 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
Praise the Lord, who [helps us] carry our heavy loads every day; he is the one who saves/rescues us.
20 Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
Our God is the God who saves us; He is Yahweh, our Lord, the one who (allows us to escape/prevents us) from being killed [in battles].
21 Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
But God will smash the heads of his enemies, the skulls of those who continue to behave sinfully.
22 Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
The Lord said, “I will bring back the [corpses of those who were killed in] Bashan, and I will bring back those who sank deep in the ocean [and drowned].
23 don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
I will do that in order that you may wash your feet in their blood, and your dogs can [also] lap up some of your enemies’ blood.”
24 Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
God, many people see you march triumphantly into your sacred temple, [celebrating that you have defeated your enemies]. You [march like] a king does, and a large crowd walks with you.
25 A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
The singers are in front, and the people who play stringed instruments are at the rear, and young women who are beating their tambourines are between them.
26 Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
[They are all singing], “You Israeli people, praise God when you gather together; praise Yahweh, all you who are descendants of Jacob!”
27 Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
First come [the people of the tribe of] Benjamin, the smallest [tribe], and following them come the leaders of [the tribe of] Judah and their group, and following them come the leaders of [the tribes of] Zebulun and Naphtali.
28 Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
God, show people that you are very powerful; show people the power with which you have helped us previously.
29 Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
Show that power from your temple in Jerusalem, where kings bring gifts to you.
30 Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
Rebuke [your enemies, such as those in Egypt who are like] wild hippopotamuses/animals that live in the reeds; and [powerful nations that are like] bulls that are among their calves [MET]; rebuke/trample them until they bow down and give you gifts of silver. Scatter the people who enjoy making wars.
31 Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
Then people will bring gifts of bronze (OR, of cloth) to you from Egypt; the people in Ethiopia will lift up their hands [to praise you].
32 Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
[You people who are citizens of] kingdoms/countries all over the world, sing to God! Sing praises to the Lord!
33 gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
Sing to the God, the one who rides across the sky, the sky that [he created] long ago. Listen as he shouts with a very powerful voice.
34 Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
Proclaim that God is very powerful; he is the king that rules over Israel, and in the skies [he also shows that] he is powerful.
35 Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!
God is awesome as he comes out of his sacred temple; he is the God whom [we] Israeli people [worship]. He makes [DOU] his people very powerful. Praise God!

< Zabura 68 >