< Zabura 68 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
“For the leader of the music. A psalm of David.” Let God arise, and his enemies are scattered, And they who hate him flee before him!
2 Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
As smoke is dispersed, so thou dispersest them; As wax melteth before the fire, So perish the wicked before the face of God.
3 Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
But the righteous are glad and rejoice in his presence, Yea, they exult exceedingly.
4 Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
Sing unto God; sing praises to his name! Prepare a way for him who rideth through the desert! Jehovah is his name; be joyful in his presence!
5 Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
The father of the fatherless, and the protector of the widow, Is God in his holy habitation.
6 Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
God causeth the forsaken to dwell in houses; He leadeth forth to prosperity them that are bound; But the rebellious shall dwell in a barren land.
7 Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
O God! when thou didst go before thy people, When thou didst march through the wilderness. (Pause)
8 duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
The earth quaked, and the heavens dropped at the presence of God; This Sinai trembled at the presence of God, the God of Israel.
9 Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
Thou, O God! didst send a plentiful rain; Thou didst strengthen thy wearied inheritance.
10 Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
Thy people established themselves in the land; Thou, O God! in thy goodness, didst prepare it for the needy!
11 Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
The Lord gave the song of victory Of the maidens publishing glad tidings to the mighty host.
12 “Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
“The kings with their armies have fled, —have fled! And the matron at home divideth the spoil.
13 Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
Truly ye may repose yourselves in the stalls, Like the wings of a dove covered with silver, And her feathers with shining gold.”
14 Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
When the Most High destroyed the kings in the land, It was white [[with their bones]] like Salmon.
15 Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
Ye lofty hills, ye hills of Bashan, Ye many-topped hills, ye hills of Bashan,
16 Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
Why frown ye, ye many-topped hills, At the hill in which God is pleased to dwell, In which Jehovah will dwell for ever?
17 Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
The chariots of God are myriads, yea, thousands of thousands; The Lord is in the midst of them, as upon Sinai, in the sanctuary.
18 Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
Thou hast ascended on high, Thou hast led captive the vanquished, Thou hast received gifts among men, Even the rebellious, that here thou mightst dwell, O LORD God!
19 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
Praised be the Lord daily! When we are heavy-laden, the Mighty One is our help.
20 Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
Our God is a God of salvation; From the Lord Jehovah cometh deliverance from death.
21 Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
But God smiteth the head of his enemies, Even the hairy crowns of those who go on in their iniquity.
22 Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
“I will bring them back,” saith the Lord, “from Bashan; I will bring them back from the deep sea;
23 don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
That thy foot may be dipped in their blood, That thy dogs may drink the blood of thine enemies.”
24 Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
We have seen thy procession, O God! The procession of my God, my king, to his sanctuary!
25 A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
The singers go before, the minstrels follow, Amidst damsels playing on timbrels.
26 Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
Praise ye God in your assemblies; Praise the Lord, all ye from the fountain of Israel!
27 Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
Here is Benjamin, the youngest, and his leaders; The chiefs of Judah, and their band; The chiefs of Zebulon, and the chiefs of Naphtali.
28 Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
Thy God has ordained thy strength, [[O Israel!]] Show forth thy might, O God! thou who hast wrought for us!
29 Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
Because of thy temple in Jerusalem Shall kings bring presents to thee.
30 Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
Rebuke the wild beast of the reeds, The multitude of bulls with the calves of the nations, So that they shall cast themselves down with masses of silver; Scatter thou the nations that delight in war!
31 Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
Princes shall come out of Egypt; Ethiopia shall haste with outstretched hands to God.
32 Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
Ye kingdoms of the earth, sing unto God; Sing praises to Jehovah;
33 gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
To him who rideth upon the ancient heaven of heavens! Behold, he uttereth his voice, his mighty voice!
34 Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
Give glory to God, Whose majesty is in Israel, and whose might is in the clouds!
35 Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!
Terrible art thou, O God! from thy sanctuary! The God of Israel giveth strength and power to his people. Praised be God!

< Zabura 68 >