< Zabura 68 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
TO THE OVERSEER. A PSALM. A SONG OF DAVID. God rises [and] His enemies are scattered! And those hating Him flee from His face.
2 Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
You drive them away as the driving away of smoke, As the melting of wax before fire, The wicked perish at the presence of God.
3 Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
And the righteous rejoice, they exult before God, And they rejoice with gladness.
4 Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
Sing to God—praise His Name, Raise up a highway for Him who is riding in deserts, In YAH [is] His Name, and exult before Him.
5 Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
Father of the fatherless, and judge of the widows, [Is] God in His holy habitation.
6 Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
God—causing the lonely to dwell at home, Bringing out bound ones into prosperity, Only—the stubborn have inhabited a dry place.
7 Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
O God, in Your going forth before Your people, In Your stepping through the wilderness, (Selah)
8 duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
The earth has shaken, Indeed, the heavens have dropped before God, This Sinai—before God, the God of Israel.
9 Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
You shake out a shower of free-will gifts, O God. Your inheritance, when it has been weary, You have established it.
10 Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
Your creature has dwelt in it, You prepare for the poor in Your goodness, O God.
11 Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
The Lord gives the saying, The female proclaimers [are] a numerous host.
12 “Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
Kings of hosts utterly flee away, And a female inhabitant of the house apportions spoil.
13 Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
Though you lie between two boundaries, Wings of a dove covered with silver, And her pinions with yellow gold.
14 Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
When the Mighty spreads kings in it, it snows in Salmon.
15 Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
A hill of God [is] the hill of Bashan, A hill of heights [is] the hill of Bashan.
16 Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
Why do you envy, O high hills, The hill God has desired for His seat? YHWH also dwells forever.
17 Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
The chariots of God [are] myriads, thousands of changes, The Lord [is] among them, in Sinai, in the sanctuary.
18 Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
You have ascended on high, You have taken captivity captive, You have taken gifts for men, That even the stubborn may rest, O YAH God.
19 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
Blessed [is] the Lord, day by day He lays on us. God Himself [is] our salvation. (Selah)
20 Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
God Himself [is] to us a God for deliverances, And YHWH Lord has the outgoings of death.
21 Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
Only—God strikes The head of His enemies, The hairy crown of a habitual walker in his guilt.
22 Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
The Lord said: “From Bashan I bring back, I bring back from the depths of the sea.
23 don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
So that you dash your foot In the blood of enemies—the tongue of Your dogs.”
24 Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
They have seen Your goings, O God, Goings of my God, my king, in the sanctuary.
25 A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
Singers have been before, Behind [are] players on instruments, Virgins playing with timbrels in the midst.
26 Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
In assemblies bless God, The Lord—from the fountain of Israel.
27 Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
There [is] little Benjamin, their ruler, Heads of Judah their defense, Heads of Zebulun—heads of Naphtali.
28 Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
Your God has commanded your strength, Be strong, O God, You have worked this for us.
29 Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
Because of Your temple at Jerusalem, Kings bring a present to You.
30 Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
Rebuke a beast of the reeds, a herd of bulls, With calves of the peoples, Each humbling himself with pieces of silver, You scatter peoples delighting in conflicts.
31 Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
Fat ones come out of Egypt, Cush causes her hands to run to God.
32 Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
Kingdoms of the earth, sing to God, Praise the Lord! (Selah)
33 gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
To Him who is riding on the heavens of the heavens of old, Behold, He gives with His voice a strong voice.
34 Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
Ascribe strength to God, His excellence [is] over Israel, and His strength in the clouds.
35 Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!
Fearful, O God, out of Your sanctuaries, The God of Israel Himself, Giving strength and might to the people. Blessed [is] God!

< Zabura 68 >