< Zabura 68 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura. Waƙa. Bari Allah yă tashi, bari a watsar da abokan gābansa; bari maƙiyansa su gudu a gabansa.
For the choirmaster. A Psalm of David. A song. God arises. His enemies are scattered, and those who hate Him flee His presence.
2 Kamar yadda iska take hura hayaƙi, bari yă hura su haka; kamar yadda kaki kan narke a gaban wuta, bari mugaye su hallaka a gaban Allah.
As smoke is blown away, You will drive them out; as wax melts before the fire, the wicked will perish in the presence of God.
3 Amma bari adalai su yi murna su kuma yi farin ciki a gaban Allah; bari su yi murna da farin ciki.
But the righteous will be glad and rejoice before God; they will celebrate with joy.
4 Rera wa Allah, rera yabo ga sunansa, ku ɗaukaka wanda yake hawa a kan gizagizai; sunansa Ubangiji ne, ku kuma yi farin ciki a gabansa.
Sing to God! Sing praises to His name. Exalt Him who rides on the clouds — His name is the LORD— and rejoice before Him.
5 Uba ga marayu, mai kāre gwauraye, shi ne Allah a mazauninsa mai tsarki.
A father of the fatherless, and a defender of the widows, is God in His holy habitation.
6 Allah ya shirya masu kaɗaici a cikin iyalai, ya jagorance’yan kurkuku da waƙoƙi; amma’yan tawaye suna zama a ƙasa mai zafin rana.
God settles the lonely in families; He leads the prisoners out to prosperity, but the rebellious dwell in a sun-scorched land.
7 Sa’ad da ka fito a gaban mutanenka, ya Allah, sa’ad da ka taka ta cikin ƙasar da take wofi, (Sela)
O God, when You went out before Your people, when You marched through the wasteland,
8 duniya ta girgiza, sammai suka zuba ruwan sama, a gaban Allah, wanda ya bayyana a Sinai, a gaban Allah, Allah na Isra’ila.
the earth shook and the heavens poured down rain before God, the One on Sinai, before God, the God of Israel.
9 Ka ba da yayyafi a yalwace, ya Allah; ka rayar da gādonka da ya gāji.
You sent abundant rain, O God; You refreshed Your weary inheritance.
10 Mutanenka suka zauna a cikinsa, kuma daga yalwarka, ya Allah, ka tanada wa matalauta.
Your flock settled therein; O God, from Your bounty You provided for the poor.
11 Ubangiji ya yi umarni, mutane masu yawa ne suka yi shelarsa,
The Lord gives the command; a great company of women proclaim it:
12 “Sarakuna da mayaƙa suka gudu a gaggauce; cikin sansani mutane sun raba ganima.
“Kings and their armies flee in haste; she who waits at home divides the plunder.
13 Har yayinda kuke barci a cikin garken tumaki, an dalaye fikafikan kurciya da azurfa, fikafikanta da zinariya mai ƙyalli.”
Though you lie down among the sheepfolds, the wings of the dove are covered with silver, and her feathers with shimmering gold.”
14 Sa’ad da Maɗaukaki ya watsar da sarakuna a cikin ƙasa, sai ya zama kamar ƙanƙara ta sauka a kan Zalmon.
When the Almighty scattered the kings in the land, it was like the snow falling on Zalmon.
15 Duwatsun Bashan, duwatsu masu alfarma ne; duwatsun Bashan masu wuyar hawa ne.
A mountain of God is Mount Bashan; a mountain of many peaks is Mount Bashan.
16 Don me kuke duba da kishi, ya duwatsu masu wuyan hawa, a kan dutsen da Allah ya zaɓa yă yi mulki, inda Ubangiji kansa zai zauna har abada?
Why do you gaze in envy, O mountains of many peaks? This is the mountain God chose for His dwelling, where the LORD will surely dwell forever.
17 Karusan Allah ninkin dubbai goma ne da kuma dubu dubbai; Ubangiji ya zo daga Sinai ya shiga cikin haikalinsa.
The chariots of God are tens of thousands— thousands of thousands are they; the Lord is in His sanctuary as He was at Sinai.
18 Sa’ad da ka hau bisa, ka bi da kamammu cikin tawagarka; ka karɓi kyautai daga mutane, har ma daga’yan tawaye, don kai, ya Ubangiji Allah, za ka zauna a can.
You have ascended on high; You have led captives away. You have received gifts from men, even from the rebellious, that the LORD God may dwell there.
19 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, ga Allah Mai Cetonmu, wanda kullum yake ɗaukan nauyinmu. (Sela)
Blessed be the Lord, who daily bears our burden, the God of our salvation.
20 Allahnmu shi ne Allah wanda yake ceto; daga Ubangiji Mai Iko Duka kuɓuta yake zuwa daga mutuwa.
Our God is a God of deliverance; the Lord GOD is our rescuer from death.
21 Tabbatacce Allah zai murƙushe kawunan abokan gābansa, rawanin gashi na waɗanda suke ci gaba cikin zunubansa.
Surely God will crush the heads of His enemies, the hairy crowns of those who persist in guilty ways.
22 Ubangiji ya ce, “Zan kawo su daga Bashan; zan kawo su daga zurfafan teku,
The Lord said, “I will retrieve them from Bashan, I will bring them up from the depths of the sea,
23 don ku wanke ƙafafunku a cikin jinin maƙiyanku, yayinda harsunan karnukanku su sami rabonsu.”
that your foot may be dipped in the blood of your foes— the tongues of your dogs in the same.”
24 Jerin gwanonka ya zo a bayyane, ya Allah, jerin gwanon Allahna da Sarkina zuwa cikin wuri mai tsarki.
They have seen Your procession, O God— the march of my God and King into the sanctuary.
25 A gaba akwai mawaƙa, a bayansu akwai makaɗa; tare da su akwai’yan mata suna bugan ganguna.
The singers lead the way, the musicians follow after, among the maidens playing tambourines.
26 Ku yabi Allah cikin taro mai girma; yabi Ubangiji cikin taron Isra’ila.
Bless God in the great congregation; bless the LORD from the fountain of Israel.
27 Ga ƙaramar kabilar Benyamin, suna jagorance su, ga babbar ƙungiya shugabannin Yahuda, ga kuma shugabannin Zebulun da na Naftali.
There is Benjamin, the youngest, ruling them, the princes of Judah in their company, the princes of Zebulun and of Naphtali.
28 Ka bayyana ikonka, ya Allah; ka nuna ƙarfinka, ya Allah, kamar yadda ka yi a dā.
Summon Your power, O God; show Your strength, O God, which You have exerted on our behalf.
29 Saboda haikalinka a Urushalima sarakuna za su kawo maka kyautai.
Because of Your temple at Jerusalem kings will bring You gifts.
30 Ka tsawata wa naman jejin nan a cikin kyauro, garken bijimai a cikin’yan maruƙan al’ummai. Ka ƙasƙantar, bari yă kawo sandunan azurfa. Ka watsar da al’ummai waɗanda suke jin daɗin yaƙi.
Rebuke the beast in the reeds, the herd of bulls among the calves of the nations, until it submits, bringing bars of silver. Scatter the nations who delight in war.
31 Jakadu za su zo daga Masar; Kush za tă miƙa kanta ga Allah.
Envoys will arrive from Egypt; Cush will stretch out her hands to God.
32 Ku rera wa Allah, ya masarautan duniya, ku rera yabo ga Ubangiji, (Sela)
Sing to God, O kingdoms of the earth; sing praises to the Lord—
33 gare shi wanda yake hawan daɗaɗɗen sararin sama, wanda yake tsawa da babbar murya.
to Him who rides upon the highest heavens of old; behold, His mighty voice resounds.
34 Ku yi shelar ikon Allah, wanda ɗaukakarsa take a bisa Isra’ila, wanda ikonsa yake a cikin sarari.
Ascribe the power to God, whose majesty is over Israel, whose strength is in the skies.
35 Kai mai banmamaki ne, ya Allah, cikin wurinka mai tsarki; Allah na Isra’ila yakan ba da iko da kuma ƙarfi ga mutanensa. Yabo ya tabbata ga Allah!
O God, You are awesome in Your sanctuary; the God of Israel Himself gives strength and power to His people. Blessed be God!