< Zabura 66 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
Emite un alegre clamor a Dios, toda la tierra:
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Haz una canción en honor de su nombre: dale alabanza y gloria.
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Di a Dios: ¡Cuánto temerán tus obras! debido a tu gran poder, sus enemigos se ven obligados a ponerse bajo sus pies.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
Deja que toda la tierra te dé culto y te haga canciones; déjalos hacer canciones a tu nombre. (Selah)
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Ven y mira las obras de Dios: debe temerse en todo lo que hace a los hijos de los hombres.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
El mar se convirtió en tierra seca; atravesaron el río a pie; allí tuvimos gozo en él.
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
Él está gobernando en el poder para siempre; sus ojos están mirando a las naciones: que sus enemigos no tengan fuerzas contra él. (Selah)
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Dan bendiciones a nuestro Dios, pueblos, la voz de su alabanza sea fuerte;
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
Porque él nos da vida, y no permitió que nuestros pies resbalen.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
Porque tú, oh Dios, nos has puesto a prueba: probándonos con fuego como la plata.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Nos dejas encarcelar; cadenas fueron puestas en nuestras piernas.
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Dejas que los hombres pasen sobre nuestras cabezas; pasamos por el fuego y el agua; pero nos sacaste a abundancia.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
Entraré en tu casa con holocaustos, pagaré mi deuda contigo,
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
Guardando la palabra que salió de mis labios, y la cual dijo mi boca, cuando estaba en problemas.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
Te daré holocaustos de animales gordos, y humo de ovejas; Haré ofrendas de bueyes y cabras. (Selah)
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Vengan, escúchenme, todos ustedes hombres temerosos de Dios, para que les aclare lo que él ha hecho por mi alma.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
Mi voz subió a él, y fui levantado del inframundo.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
Dije en mi corazón: Jehová no me escuchará:
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
Pero verdaderamente el oído de Dios ha sido abierto; él ha prestado atención a la voz de mi oración.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Alabado sea Dios que no me ha quitado su buena fe y su misericordia.

< Zabura 66 >