< Zabura 66 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
Aclame a ʼElohim, toda la tierra.
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Canten la gloria de su Nombre. Hagan gloriosa su alabanza.
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Digan a ʼElohim: ¡Cuán asombrosas son tus obras! Por la grandeza de tu poder Se someterán a Ti tus enemigos.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
Toda la tierra te adorará Y cantará alabanzas a Ti. Cantarán salmos a tu Nombre. (Selah)
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Vengan y contemplen las obras de ʼElohim, Admirable en sus hechos para los hijos de [los] hombres.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
Convirtió el mar en tierra seca. Por el río pasaron a pie. Allí nos regocijamos en Él.
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
Él gobierna con su poder para siempre. Sus ojos vigilan las naciones. No se enaltezcan los rebeldes. (Selah)
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Bendigan, pueblos, a nuestro ʼElohim, Y proclamen la voz de su alabanza.
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
Él preserva la vida a nuestra alma Y no permite que resbale nuestro pie.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
Porque Tú nos probaste, oh ʼElohim. Nos purificaste en el crisol como se purifica la plata.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Nos metiste en la red. Pusiste sobre nuestra cintura una carga muy pesada.
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Ordenaste que los hombres cabalgaran sobre nuestras cabezas. Pasamos por el fuego y por el agua. Pero luego nos sacaste a la abundancia.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
Entraré en tu Casa con holocaustos. Te pagaré mis votos
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
Que pronunciaron mis labios, Que mi boca dijo cuando estaba angustiado.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
Te ofreceré holocaustos engordados con el humo de carneros. Te ofreceré becerros y machos cabríos. (Selah)
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Vengan, escuchen todos los que temen a ʼElohim Y relataré lo que hizo por mi vida.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
A Él clamé con mi boca, Y Él fue exaltado con mi lengua.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
Si en mi corazón tuviera yo iniquidad ʼAdonay no me habría escuchado.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
Pero ciertamente ʼElohim me escuchó Y atendió la voz de mi súplica.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Bendito sea ʼElohim, Quien no desechó mi oración, Ni apartó de mí su misericordia.

< Zabura 66 >