< Zabura 66 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
В конец, песнь псалма воскресения.
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Воскликните Господеви вся земля, пойте же имени Его, дадите славу хвале Его.
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Рцыте Богу: коль страшна дела Твоя? Во множестве силы Твоея солжут Тебе врази Твои.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
Вся земля да поклонится Тебе и поет Тебе, да поет же имени Твоему, Вышний.
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Приидите и видите дела Божия, коль страшен в советех паче сынов человеческих.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
Обращаяй море в сушу, в реце пройдут ногами: тамо возвеселимся о Нем,
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
владычествующем силою Своею веком: очи Его на языки призираете: преогорчевающии да не возносятся в себе.
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Благословите, языцы, Бога нашего, и услышан сотворите глас хвалы Его,
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
положшаго душу мою в живот, и не давшаго во смятение ног моих.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
Яко искусил ны еси, Боже, разжегл ны еси, якоже разжизается сребро.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Ввел ны еси в сеть, положил еси скорби на хребте нашем.
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Возвел еси человеки на главы нашя: проидохом сквозе огнь и воду, и извел еси ны в покой.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
Вниду в дом Твой со всесожжением, воздам Тебе молитвы моя,
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
яже изрекосте устне мои, и глаголаша уста моя в скорби моей.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
Всесожжения тучна вознесу Тебе с кадилом, и овны, вознесу Тебе волы с козлы.
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Приидите, услышите, и повем вам, вси боящиися Бога, елика сотвори души моей.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
К Нему усты моими воззвах, и вознесох под языком моим.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
Неправду аще узрех в сердцы моем, да не услышит мене Господь.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
Сего ради услыша мя Бог, внят гласу моления моего.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Благословен Бог, Иже не отстави молитву мою и милость Свою от мене.