< Zabura 66 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
in finem canticum psalmi resurrectionis iubilate Deo omnis terra
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
psalmum dicite nomini eius date gloriam laudi eius
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
dicite Deo quam terribilia sunt opera tua Domine in multitudine virtutis tuae mentientur tibi inimici tui
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
omnis terra adorent te et psallant tibi psalmum dicant nomini tuo diapsalma
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
venite et videte opera Dei terribilis in consiliis super filios hominum
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
qui convertit mare in aridam in flumine pertransibunt pede ibi laetabimur in ipso
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
qui dominatur in virtute sua in aeternum oculi eius super gentes respiciunt qui exasperant non exaltentur in semet ipsis diapsalma
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
benedicite gentes Deum nostrum et auditam facite vocem laudis eius
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
qui posuit animam meam ad vitam et non dedit in commotionem pedes meos
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
quoniam probasti nos Deus igne nos examinasti sicut examinatur argentum
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
induxisti nos in laqueum posuisti tribulationes in dorso nostro
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
inposuisti homines super capita nostra transivimus per ignem et aquam et eduxisti nos in refrigerium
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
introibo in domum tuam in holocaustis reddam tibi vota mea
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
quae distinxerunt labia mea et locutum est os meum in tribulatione mea
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
holocausta medullata offeram tibi cum incensu arietum offeram tibi boves cum hircis diapsalma
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
venite audite et narrabo omnes qui timetis Deum quanta fecit animae meae
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
ad ipsum ore meo clamavi et exaltavi sub lingua mea
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
iniquitatem si aspexi in corde meo non exaudiat Dominus
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
propterea exaudivit Deus adtendit voci deprecationis meae
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
benedictus Deus qui non amovit orationem meam et misericordiam suam a me