< Zabura 66 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
Dem Musikmeister; ein Lied, ein Psalm. Jauchzet Gott, ihr Lande alle!
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Lobsinget der Ehre seines Namens,
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Sprechet zu Gott: »Wie wunderbar ist dein Walten! Ob der Fülle deiner Macht huldigen dir sogar deine Feinde.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
Alle Lande müssen vor dir sich niederwerfen und dir lobsingen, lobsingen deinem Namen!« (SELA)
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Kommt und schauet die Großtaten Gottes, der wunderbar ist im Walten über den Menschenkindern!
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
Er wandelte das Meer in trocknes Land, so daß man den Strom zu Fuß durchzog; drum wollen wir uns freun!
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
Ewig herrscht er in seiner Macht; seine Augen haben acht auf die Völker: die Widerspenstigen dürfen sich nicht stolz erheben. (SELA)
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Preiset, ihr Völker, unsern Gott, laßt laut seinen Ruhm erschallen,
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
ihn, der unsre Seele am Leben erhalten und unsern Fuß nicht hat wanken lassen.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
Wohl hast du uns geprüft, o Gott, uns geläutert, wie man Silber läutert;
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
du hast uns ins Netz geraten lassen, hast drückende Last auf unsern Rücken gelegt;
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Menschen hast du hinfahren lassen über unser Haupt, durch Feuer und Wasser haben wir ziehen müssen: doch endlich hast du uns ins Freie hinausgeführt.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
Ich komme mit Brandopfern in dein Haus, entrichte dir meine Gelübde,
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
zu denen meine Lippen sich verpflichtet haben, und die mein Mund verheißen in meiner Not.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
Brandopfer von Mastvieh will ich dir bringen samt dem Opferduft von Widdern; Rinder samt Böcken will ich zubereiten. (SELA)
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Kommt her und höret, ihr Gottesfürchtigen alle: ich will erzählen, was er an meiner Seele getan!
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
Zu ihm hab’ ich laut mit meinem Munde gerufen, während Lobpreis schon auf meiner Zunge lag.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
Wäre mein Sinn auf Böses gerichtet gewesen, so hätte der Allherr mich nicht erhört.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
Aber Gott hat mich erhört, hat geachtet auf mein lautes Flehen.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Gepriesen sei Gott, der mein Flehen nicht verworfen und seine Gnade mir nicht versagt hat!