< Zabura 66 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
Cantique d’un psaume de résurrection. Poussez des cris de joie vers Dieu, ô terre tout entière;
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Dites un psaume à l’honneur de son nom: rendez gloire à sa louange.
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Dites à Dieu: Que vos œuvres sont redoutables, Seigneur! à la vue de la grandeur de votre puissance, vos ennemis vous mentiront.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
Que toute la terre vous adore et vous chante; qu’elle dise un psaume à la gloire de votre nom.
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Venez et voyez les œuvres de Dieu: il est terrible dans ses desseins sur les fils des hommes.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
C’est lui qui a changé la mer en une terre aride: ils passeront dans un fleuve à pied sec, là nous nous réjouirons.
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
C’est lui qui domine éternellement par sa puissance: ses yeux regardent les nations: que ceux qui l’irritent ne s’élèvent pas en eux-mêmes.
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Bénissez, ô nations, notre Dieu, faites entendre la voix de sa louange.
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
C’est lui qui a rendu mon âme à la vie, et qui n’a pas permis que mes pieds aient chancelé.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
Parce que vous nous avez éprouvés, ô Dieu, vous nous avez épurés par le feu, comme l’argent est épuré.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Vous nous avez conduits dans le lacs, vous avez mis des tribulations sur nos épaules:
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Vous avez imposé des hommes sur nos têtes.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
J’entrerai dans votre maison avec des holocaustes; je vous rendrai mes vœux,
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
Qu’ont proférés mes lèvres, Et qu’a exprimés ma bouche dans ma tribulation.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
Je vous offrirai des holocaustes gras, avec la fumée des béliers: je vous offrirai des bœufs avec des boucs.
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Venez et écoutez, vous tous qui craignez le Dieu Seigneur, et je raconterai quelles grandes choses il a faites pour mon âme.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
C’est vers lui que j’ai crié de ma bouche, et c’est lui que j’ai exalté par ma langue.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
Si j’ai regardé l’iniquité dans mon cœur, le Seigneur ne m’exaucera pas.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
C’est pour cela que le Seigneur m’a exaucé, et qu’il a été attentif à la voix de ma supplication.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Béni le Dieu qui n’a pas écarté ma prière, ni sa miséricorde de moi!