< Zabura 66 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Chantez la gloire de son nom; louez-le, et lui rendez gloire!
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Dites à Dieu: Que tes œuvres sont redoutables! A cause de la grandeur de ta force, tes ennemis viendront se soumettre à toi.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
Toute la terre se prosternera devant toi; elle chantera en ton honneur, elle chantera ton nom. (Sélah)
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Venez, et voyez les œuvres de Dieu; il est redoutable dans ce qu'il fait envers les fils des hommes.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
Il a changé la mer en terre sèche; on passait à pied dans le fleuve; là nous nous sommes réjouis en lui.
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
Il domine éternellement par sa puissance; ses yeux observent les nations, pour que les rebelles ne s'élèvent pas. (Sélah)
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Peuples, bénissez notre Dieu, et faites entendre la voix de sa louange!
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
Lui qui a conservé la vie à notre âme, et qui n'a pas permis que nos pieds bronchassent.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
Car tu nous as éprouvés, ô Dieu; tu nous as fait passer au creuset comme l'argent.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Tu nous avais amenés dans le filet; tu avais mis sur nos reins un pesant fardeau;
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Tu avais fait monter les hommes sur nos têtes; nous étions entrés dans le feu et dans l'eau; mais tu nous as mis au large et dans l'abondance.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
J'entrerai dans ta maison avec des holocaustes; et je te rendrai mes vœux,
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
Que mes lèvres ont proférés et que ma bouche a prononcés dans ma détresse.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
Je t'offrirai des brebis grasses en holocauste, avec les béliers fumant sur l'autel; je sacrifierai des taureaux avec des boucs. (Sélah)
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Vous tous qui craignez Dieu, venez, écoutez, et je raconterai ce qu'il a fait à mon âme.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
Je l'ai invoqué de ma bouche; aussi ma langue l'exaltera.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
Si j'eusse pensé quelque iniquité dans mon cœur, le Seigneur ne m'eût point écouté.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
Mais certainement Dieu m'a écouté; il a prêté l'oreille à la voix de ma prière.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Béni soit Dieu qui n'a point rejeté ma prière, ni retiré de moi sa bonté!