< Zabura 66 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
Jusqu'à la Fin, psaume de la Résurrection. Terre, jette tout entière des cris de joie au Seigneur.
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Chantez des louanges en son nom; rendez gloire à sa louange;
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Dites à Dieu: Que tes œuvres sont redoutables, Seigneur! tes ennemis seront contraints, par la plénitude de ta puissance, à feindre devant toi.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
Que toute la terre t'adore; qu'elle chante vers toi; qu'elle chante à ton nom.
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Venez et voyez les œuvres du Seigneur; il est redoutable en ses conseils, sur les fils des hommes.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
Il change la mer en une plage aride; on traversera le fleuve à pied. Là nous nous réjouirons en lui,
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
Qui en sa force est le maître de toute éternité. Ses yeux regardent les nations; que ceux qui l'irritent ne s'exaltent point en eux-mêmes.
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Nations, bénissez notre Dieu, et faites retentir la voix de sa louange.
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
C'est lui qui a vivifié mon âme, et qui n'a point permis que mes pieds soient ébranlés.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
Tu nous as éprouvés, ô Dieu; tu nous as purifiés par le feu, comme l'argent.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Tu nous as conduits en un piège; tu as chargé nos épaules d'affliction.
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Tu as fait monter des hommes sur nos têtes; nous avons passé à travers l'eau et le feu, et tu nous as amenés en un lieu de rafraîchissement.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
J'entrerai dans ta demeure avec des holocaustes; je te rendrai les vœux
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
Que mes lèvres ont proférés; et ma bouche a parlé en mon affliction.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
Je t'offrirai des holocaustes pleins de moelle, avec de l'encens et des béliers; je te sacrifierai des bœufs et des chèvres.
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Ô vous qui craignez le Seigneur, vous tous écoutez, et je dirai que de grandes choses il a faites pour mon âme.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
J'ai crié vers lui de ma bouche; je l'ai glorifié de ma langue.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
Si, en mon cœur, j'ai connu l'iniquité, que le Seigneur ne m'exauce jamais.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
A cause de cela, le Seigneur m'a écouté; il a été attentif à la voix de ma prière.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Béni soit Dieu qui n'a jamais rejeté ma prière et n'a point détourné de moi sa miséricorde.

< Zabura 66 >