< Zabura 66 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
Au chef des chantres. Cantique. Psaume. Que toute la terre acclame Dieu!
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Chantez la gloire de son nom, faites de ses louanges un tribut d’honneur.
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Dites à Dieu: "Que tes œuvres sont prodigieuses! A cause de ta toute-puissance tes ennemis rampent devant toi;
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
la terre entière se prosterne à tes pieds, entonne tes louanges, célèbre ton nom." (Sélah)
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Venez et contemplez les hauts faits de Dieu! Merveilleuse est son action sur les fils de l’homme.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
Il change la mer en terre ferme, à travers le fleuve on marche à pied sec; dès lors nous mîmes notre joie en lui.
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
Il règne éternellement dans sa force, ses regards observent les nations: que les rebelles ne portent pas le front haut! (Sélah)
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Nations, bénissez notre Dieu, faites retentir le bruit de ses louanges!
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
Il nous a gratifiés de la vie, et n’a pas laissé nos pieds chanceler.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
Car tu nous as éprouvés, ô notre Dieu, jetés au creuset comme on fait de l’argent.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Tu nous avais amenés dans un filet, tu avais chargé nos reins d’un pesant fardeau,
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
courbé notre tête sous le joug des gens. Nous avions passé par le feu et par l’eau; mais tu nous as remis dans l’abondance.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
Je me présenterai dans ta maison avec des holocaustes, pour m’acquitter envers toi de tous mes vœux,
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
que mes lèvres ont exprimés, qu’au cours de ma détresse ma bouche a formulés.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
Je t’offrirai des brebis grasses comme holocaustes, avec la fumée des béliers; j’immolerai des taureaux ainsi que des boucs. (Sélah)
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Venez et écoutez: Je veux raconter, ô vous tous qui craignez Dieu, ce qu’il a fait en ma faveur!
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
A pleine bouche je l’avais invoqué, il se trouvait exalté par mes lèvres.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
Si, dans mon cœur, j’avais eu en vue l’iniquité, Dieu ne m’eût pas entendu.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
Eh bien! Dieu a entendu; il a été attentif aux accents de ma prière.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Loué soit Dieu qui n’a pas repoussé ma prière, et ne m’a pas retiré sa grâce!

< Zabura 66 >