< Zabura 66 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
To the Overseer. — A Song, a Psalm. Shout ye to God, all the earth.
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Praise ye the honour of His name, Make ye honourable His praise.
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Say to God, 'How fearful [are] Thy works, By the abundance of Thy strength, Thine enemies feign obedience to Thee.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
All the earth do bow to Thee, They sing praise to Thee, they praise Thy name.' (Selah)
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Come ye, and see the works of God, Fearful acts toward the sons of men.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
He hath turned a sea to dry land, Through a river they pass over on foot, There do we rejoice in Him.
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
Ruling by His might to the age, His eyes among the nations do watch, The refractory exalt not themselves. (Selah)
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Bless, ye peoples, our God, And sound the voice of His praise,
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
Who hath placed our soul in life, And suffered not our feet to be moved.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
For Thou hast tried us, O God, Thou hast refined us as the refining of silver.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Thou hast brought us into a net, Thou hast placed pressure on our loins.
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Thou hast caused man to ride at our head. We have entered into fire and into water, And Thou bringest us out to a watered place.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
I enter Thy house with burnt-offerings, I complete to Thee my vows,
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
For opened were my lips, And my mouth spake in my distress:
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
'Burnt-offerings of fatlings I offer to Thee, With perfume of rams, I prepare a bullock with he-goats.' (Selah)
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Come, hear, all ye who fear God, And I recount what he did for my soul.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
Unto Him [with] my mouth I have called, And exaltation [is] under my tongue.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
Iniquity, if I have seen in my heart, The Lord doth not hear.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
But God hath heard, He hath attended to the voice of my prayer.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Blessed [is] God, Who hath not turned aside my prayer, And His loving-kindness, from me!

< Zabura 66 >