< Zabura 66 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
For the end, a Song of Psalm of resurrection. Shout to God, all the earth.
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
O sing praises to his name; give glory to his praise.
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Say to God, How awful are your works! through the greatness of your power your enemies shall lie to you.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
Let all the earth worship you, and sing to you; let them sing to your name. (Pause)
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Come and behold the works of God; [he is] terrible in [his] counsels beyond the children of men.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
Who turns the sea into dry land; they shall go through the river on foot; there shall we rejoice in him,
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
who by his power is Lord over the age, his eyes look upon the nations; let not them that provoke [him] be exalted in themselves. (Pause)
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Bless our God, you Gentiles, and make the voice of his praise to be heard;
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
who quickens my soul in life, and does not suffer my feet to be moved.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
For you, O God, has proved us; you have tried us with fire as silver is tried.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
You brought us into the snare; you laid afflictions on our back.
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
You did mount men upon our heads; we went through the fire and water; but you brought us out into [a place of] refreshment.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
I will go into your house with whole burnt offerings; I will pay you my vows,
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
which my lips framed, and my mouth uttered in my affliction.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
I will offer to you whole burnt sacrifices full of marrow, with incense and rams; I will sacrifice to you oxen with goats. (Pause)
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Come, hear, and I will tell, all you that fear God, how great things he has done for my soul.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
I cried to him with my mouth, and exalted him with my tongue.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
If I have regarded iniquity in my heart, let not the Lord listen [to me].
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
Therefore God has listened to me; he has attended to the voice of my prayer.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Blessed be God, who has not turned away my prayer, nor his mercy from me.