< Zabura 66 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
Unto the end, a canticle of a psalm of the resurrection. Shout with joy to God, all the earth,
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Sing ye a psalm to his name; give glory to his praise.
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Say unto God, How terrible are thy works, O Lord! in the multitude of thy strength thy enemies shall lie to thee.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
Let all the earth adore thee, and sing to thee: let it sing a psalm to thy name.
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Come and see the works of God; who is terrible in his counsels over the sons of men.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
Who turneth the sea into dry land, in the river they shall pass on foot: there shall we rejoice in him.
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
Who by his power ruleth for ever: his eyes behold the nations; let not them that provoke him he exalted in themselves.
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
O bless our God, ye Gentiles: and make the voice of his praise to be heard.
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
Who hath set my soul to live: and hath not suffered my feet to be moved:
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
For thou, O God, hast proved us: thou hast tried us by fire, as silver is tried.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Thou hast brought us into a net, thou hast laid afflictions on our back:
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Thou hast set men over our heads. We have passed through tire and water, and thou hast brought us out into a refreshment.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
I will go into thy house with burnt offerings: I will pay thee my vows,
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
Which my lips have uttered, And my mouth hath spoken, when I was in trouble.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
I will offer up to thee holocausts full of marrow, with burnt offerings of rams: I will offer to thee bullocks with goats.
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Come and hear, all ye that fear God, and I will tell you what great things he hath done for my soul.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
I cried to him with my mouth: and I extolled him with my tongue.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
If I have looked at iniquity in my heart, the Lord will not hear me.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
Therefore hath God heard me, and hath attended to the voice of my supplication.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Blessed be God, who hath not turned away my prayer, nor his mercy from me.