< Zabura 66 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
To the chief Musician. A Song: a Psalm. Shout aloud unto God, all the earth:
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Sing forth the glory of his name, make his praise glorious;
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Say unto God, How terrible are thy works! because of the greatness of thy strength, thine enemies come cringing unto thee.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
All the earth shall worship thee, and sing psalms unto thee: they shall sing forth thy name. (Selah)
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Come and see the works of God: he is terrible in [his] doings toward the children of men.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
He turned the sea into dry [land]; they went through the river on foot: there did we rejoice in him.
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
He ruleth by his power for ever; his eyes observe the nations: let not the rebellious exalt themselves. (Selah)
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
Bless our God, ye peoples, and make the voice of his praise to be heard;
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
Who hath set our soul in life, and suffereth not our feet to be moved.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
For thou, O God, hast proved us: thou hast tried us, as silver is tried.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Thou broughtest us into a net, thou didst lay a heavy burden upon our loins;
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Thou didst cause men to ride over our head; we went through fire and through water: but thou hast brought us out into abundance.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
I will go into thy house with burnt-offerings; I will perform my vows to thee,
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
Which my lips have uttered, and my mouth hath spoken, when I was in trouble.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
I will offer up unto thee burnt-offerings of fatted beasts, with the incense of rams; I will offer bullocks with goats. (Selah)
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Come, hear, all ye that fear God, and I will declare what he hath done for my soul.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
I called unto him with my mouth, and he was extolled with my tongue.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
Had I regarded iniquity in my heart, the Lord would not hear.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
But God hath heard; he hath attended to the voice of my prayer.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Blessed be God, who hath not turned away my prayer, nor his loving-kindness from me!