< Zabura 66 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
Make a joyful noise to God, all the earth.
2 Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
Sing forth the glory of his name. Make his praise glorious.
3 Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
Say to God, How awesome are thy works! Through the greatness of thy power thine enemies shall submit themselves to thee.
4 Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
All the earth shall worship thee, and shall sing to thee. They shall sing to thy name. (Selah)
5 Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
Come, and see the works of God, awesome in actions toward the sons of men.
6 Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
He turned the sea into dry land. They went through the river on foot. There we rejoiced in him.
7 Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
He rules by his might forever. His eyes observe the nations. Let not the rebellious exalt themselves. (Selah)
8 Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
O bless our God, ye peoples, and make the voice of his praise to be heard,
9 ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
who holds our soul in life, and does not allow our feet to be moved.
10 Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
For thou, O God, have proved us. Thou have tried us as silver is tried.
11 Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
Thou brought us into the net. Thou laid a great burden upon our loins.
12 Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
Thou caused men to ride over our heads. We went through fire and through water. But thou brought us out into a wealthy place.
13 Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
I will come into thy house with burnt offerings. I will pay thee my vows,
14 alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
which my lips uttered, and my mouth spoke, when I was in distress.
15 Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
I will offer to thee burnt offerings of fatlings, with the incense of rams. I will offer bullocks with goats. (Selah)
16 Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
Come, and hear, all ye who fear God, and I will declare what he has done for my soul.
17 Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
I cried to him with my mouth, and he was extolled with my tongue.
18 Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
If I regard iniquity in my heart, the Lord will not hear.
19 amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
But truly God has heard. He has attended to the voice of my prayer.
20 Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!
Blessed be God, who has not turned away my prayer, nor his loving kindness from me.

< Zabura 66 >