< Zabura 65 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Wata waƙa. Yabo ya dace da kai, ya Allah, a Sihiyona; a gare ka za mu cika alkawuranmu
Psaume de David, [qui est] un Cantique, [donné] au maître chantre. Ô Dieu! la louange t'[attend] dans le silence en Sion, et le vœu te sera rendu.
2 Ya kai wanda yake jin addu’a a gare ka dukan mutane za su zo.
Tu y entends les requêtes, toute créature viendra jusqu'à toi.
3 Sa’ad da zunubai suka sha ƙarfinmu, ka gafarta laifofinmu.
Les iniquités avaient prévalu sur moi, [mais] tu feras l'expiation de nos transgressions.
4 Masu albarka ne waɗanda ka zaɓa ka kawo kusa don su zauna a filayenka! Mun cika da abubuwa masu kyau na gidanka, na haikalinka mai tsarki.
Ô que bienheureux est celui que tu auras choisi et que tu auras fait approcher, afin qu'il habite dans tes parvis! Nous serons rassasiés des biens de ta maison, des biens du saint lieu de ton palais.
5 Ka amsa mana da ayyuka masu banmamaki na adalci, Ya Allah Mai Cetonmu, begen dukan iyakar duniya da kuma na tekuna masu nesa,
Ô Dieu de notre délivrance, tu nous répondras par des choses terribles, [faites] avec justice, toi qui es l'assurance de tous les bouts de la terre, et des plus éloignés de la mer.
6 wanda ya yi duwatsu ta wurin ikonka, bayan ka kintsa kanka da ƙarfi,
Il tient fermes les montagnes par sa force, [et] il est ceint de puissance.
7 wanda ya kwantar da rurin tekuna, rurin raƙumansu, da kuma tumbatsar al’ummai.
Il apaise le bruit de la mer, le bruit de ses ondes, et l'émotion des peuples.
8 Waɗanda suke zama can da nesa sukan ji tsoron manyan ayyukanka; inda safe ke haskaka yamma kuma ta shuɗe kakan sa a yi waƙoƙin farin ciki.
Et ceux qui habitent aux bouts de la terre ont peur de tes prodiges; tu réjouis l'Orient et l'Occident.
9 Kana kula da ƙasa kana kuma yi mata banruwa; kana azurta ta a yalwace. Rafuffukan Allah sun cika da ruwa don su ba mutane hatsi, don haka ne ka ƙaddara.
Tu visites la terre, [et] après que tu l'as rendue altérée, tu l'enrichis amplement; le ruisseau de Dieu est plein d'eau; tu prépares leurs blés, après que tu l'as ainsi disposée.
10 Ka kwarara ta da ruwa ka kuma baje kunyoyinta; ka sa ta yi laushi da yayyafi ka kuma albarkaci tsire-tsirenta.
Tu arroses ses sillons, et tu aplanis ses rayons; tu l'amollis par la pluie menue, et tu bénis son germe.
11 Saboda alherinka, ya Allah, an sami kaka mai albarka, amalankenka kuwa sun cika har suna zuba.
Tu couronnes l'année de tes biens, et tes ornières font couler la graisse.
12 Makiyayan hamada sun cika har suna zuba; tuddai sun rufu da murna.
Elles la font couler sur les loges du désert, et les côteaux sont ceints de joie.
13 Wurin dausayin kiwo sun rufu da garkuna kwari kuma sun cika da hatsi; suna sowa don farin ciki.
Les campagnes sont revêtues de troupeaux, et les vallées sont couvertes de froment; elles en triomphent, et elles en chantent.