< Zabura 65 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Wata waƙa. Yabo ya dace da kai, ya Allah, a Sihiyona; a gare ka za mu cika alkawuranmu
Au chef de musique. Psaume de David. Cantique. Ô Dieu! la louange t’attend dans le silence en Sion, et le vœu te sera payé.
2 Ya kai wanda yake jin addu’a a gare ka dukan mutane za su zo.
Ô toi qui écoutes la prière! toute chair viendra à toi.
3 Sa’ad da zunubai suka sha ƙarfinmu, ka gafarta laifofinmu.
Les iniquités ont prévalu sur moi; nos transgressions, toi tu les pardonneras.
4 Masu albarka ne waɗanda ka zaɓa ka kawo kusa don su zauna a filayenka! Mun cika da abubuwa masu kyau na gidanka, na haikalinka mai tsarki.
Bienheureux celui que tu as choisi et que tu fais approcher: il habitera tes parvis. Nous serons rassasiés du bien de ta maison, de ton saint temple.
5 Ka amsa mana da ayyuka masu banmamaki na adalci, Ya Allah Mai Cetonmu, begen dukan iyakar duniya da kuma na tekuna masu nesa,
Tu nous répondras par des choses terribles de justice, ô Dieu de notre salut, toi qui es la confiance de tous les bouts de la terre, et des régions lointaines de la mer!
6 wanda ya yi duwatsu ta wurin ikonka, bayan ka kintsa kanka da ƙarfi,
Toi qui as établi les montagnes par ta force, qui es ceint de puissance,
7 wanda ya kwantar da rurin tekuna, rurin raƙumansu, da kuma tumbatsar al’ummai.
Qui apaises le tumulte des mers, le tumulte de leurs flots, et l’agitation des peuplades.
8 Waɗanda suke zama can da nesa sukan ji tsoron manyan ayyukanka; inda safe ke haskaka yamma kuma ta shuɗe kakan sa a yi waƙoƙin farin ciki.
Et ceux qui habitent aux bouts [de la terre] craindront à la vue de tes prodiges; tu fais chanter de joie les sorties du matin et du soir.
9 Kana kula da ƙasa kana kuma yi mata banruwa; kana azurta ta a yalwace. Rafuffukan Allah sun cika da ruwa don su ba mutane hatsi, don haka ne ka ƙaddara.
Tu as visité la terre, tu l’as abreuvée, tu l’enrichis abondamment: le ruisseau de Dieu est plein d’eau. Tu prépares les blés, quand tu l’as ainsi préparée.
10 Ka kwarara ta da ruwa ka kuma baje kunyoyinta; ka sa ta yi laushi da yayyafi ka kuma albarkaci tsire-tsirenta.
Tu arroses ses sillons, tu aplanis ses mottes, tu l’amollis par des ondées, tu bénis son germe.
11 Saboda alherinka, ya Allah, an sami kaka mai albarka, amalankenka kuwa sun cika har suna zuba.
Tu couronnes l’année de ta bonté, et tes sentiers distillent la graisse.
12 Makiyayan hamada sun cika har suna zuba; tuddai sun rufu da murna.
Ils distillent sur les pâturages du désert, et les collines se ceignent d’allégresse.
13 Wurin dausayin kiwo sun rufu da garkuna kwari kuma sun cika da hatsi; suna sowa don farin ciki.
Les prairies se revêtent de menu bétail, et les plaines sont couvertes de froment: elles poussent des cris de triomphe; oui, elles chantent.