< Zabura 65 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Wata waƙa. Yabo ya dace da kai, ya Allah, a Sihiyona; a gare ka za mu cika alkawuranmu
“For the leader of the music. A psalm of David.” To thee belongeth trust, to thee praise, O God in Zion! And to thee shall the vow be performed!
2 Ya kai wanda yake jin addu’a a gare ka dukan mutane za su zo.
O Thou that hearest prayer! To thee shall all flesh come!
3 Sa’ad da zunubai suka sha ƙarfinmu, ka gafarta laifofinmu.
My iniquities are heavy upon me; But thou wilt forgive our transgressions!
4 Masu albarka ne waɗanda ka zaɓa ka kawo kusa don su zauna a filayenka! Mun cika da abubuwa masu kyau na gidanka, na haikalinka mai tsarki.
Happy is he whom thou choosest, And bringest near thee to dwell in thy courts! May we be satisfied with the blessings of thy house, Thy holy temple!
5 Ka amsa mana da ayyuka masu banmamaki na adalci, Ya Allah Mai Cetonmu, begen dukan iyakar duniya da kuma na tekuna masu nesa,
By wonderful deeds dost thou answer us in thy goodness, O God, our salvation! Who art the confidence of all the ends of the earth, And of the most distant seas!
6 wanda ya yi duwatsu ta wurin ikonka, bayan ka kintsa kanka da ƙarfi,
Thou makest fast the mountains by thy power, Being girded with strength!
7 wanda ya kwantar da rurin tekuna, rurin raƙumansu, da kuma tumbatsar al’ummai.
Thou stillest the roar of the sea, The roar of its waves, And the tumult of the nations.
8 Waɗanda suke zama can da nesa sukan ji tsoron manyan ayyukanka; inda safe ke haskaka yamma kuma ta shuɗe kakan sa a yi waƙoƙin farin ciki.
They who dwell in the ends of the earth are awed by thy signs; Thou makest the outgoings of the morning and of the evening to rejoice!
9 Kana kula da ƙasa kana kuma yi mata banruwa; kana azurta ta a yalwace. Rafuffukan Allah sun cika da ruwa don su ba mutane hatsi, don haka ne ka ƙaddara.
Thou visitest the earth and waterest it; Thou enrichest it exceedingly; The river of God is full of water. Thou suppliest the earth with corn, When thou hast thus prepared it.
10 Ka kwarara ta da ruwa ka kuma baje kunyoyinta; ka sa ta yi laushi da yayyafi ka kuma albarkaci tsire-tsirenta.
Thou waterest its furrows, And breakest down its ridges; Thou makest it soft with showers, And blessest its increase.
11 Saboda alherinka, ya Allah, an sami kaka mai albarka, amalankenka kuwa sun cika har suna zuba.
Thou crownest the year with thy goodness; Thy footsteps drop fruitfulness;
12 Makiyayan hamada sun cika har suna zuba; tuddai sun rufu da murna.
They drop it upon the pastures of the wilderness, And the hills are girded with gladness.
13 Wurin dausayin kiwo sun rufu da garkuna kwari kuma sun cika da hatsi; suna sowa don farin ciki.
The pastures are clothed with flocks, And the valleys are covered with corn; They shout, yea, they sing for joy.

< Zabura 65 >