< Zabura 64 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
Для дириґента хору. Псалом Давидів. Вислухай, Боже, мій голос, як ска́ржуся я, від стра́ху ворожого душу мою хорони!
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
Заховай мене від потає́много збору злочинців, від крику сваві́льців,
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
які нагостри́ли свого язика́, як меча, натягнули стрілу́ свою словом гірки́м,
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
щоб таємно стріляти в невинного, — вони нагло стріля́тимуть в нього, і не бу́дуть боятись!
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
У злій справі зміцня́ють себе, змовля́ються па́стки таємно розста́вити, кажуть: „Хто бу́де їх бачити?“
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
Вони кривди ховають. Загинемо, як за́дум їхній спо́вниться, бо нутро́ чоловіка та серце — глибоке!
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
Але́ вчинить Бог, що стріла́ на них стрі́лить, — і на́гло пора́нені будуть,
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
і вчинить, що їхній язик допаде́ться до них, — і будуть хита́ти головою усі, хто спогля́не на них!
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
І всі люди боятися будуть, і будуть розказувати про чин Бога, і ді́ло Його зрозуміють!
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
І праведний Господом бу́де раді́ти, і буде вдава́тись до Нього, і бу́дуть похва́лені всі простосе́рді!