< Zabura 64 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
Escucha, oh ʼElohim, la voz de mi queja: Preserva mi vida del terror de perversos.
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
Ocúltame de la conspiración de malhechores, Del tumulto de los que hacen iniquidad,
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
Que afilan sus lenguas como una espada, Y la emplean como su flecha en un lenguaje amargo
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
Para dispararlas en oculto al inocente. De repente disparan sus flechas, sin que teman.
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
Se animan unos a otros en su perverso designio Y planean esconder trampas. Dicen: ¿Quién las verá?
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
Traman injusticias y dicen: Estamos listos con una conspiración bien concebida. Tanto el pensamiento íntimo como el corazón del hombre son profundos.
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
Pero ʼElohim les dispara una flecha. De repente vendrán sus plagas.
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
Así que ellas los hacen tropezar. Los que los ven menean la cabeza.
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
Entonces temerán todos los hombres. Proclamarán la obra de ʼElohim Y entenderán sus hechos.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
El justo se alegrará en Yavé, Y se confiará en Él. Se gloriarán todos los rectos de corazón.

< Zabura 64 >