< Zabura 64 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
MAIN Kot, kotin ereki nil ai ni ai injenjued. Kom kotin jinjila maur i mon ai imwintiti weit.
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
Kom kotin karuki ia la jan mon pokon en me jued akan, mon pwin en me wia japun kan.
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
Me kin ada lo’rail dueta kodlaj pot, o me kaonopada ar kajik katieu, iei ar lokaia jued,
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
Pwen rir kajikiedi me lelapok o; madan re pan kajikiedi i, o jota injenoki.
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
Irail me weit ni ar tiak jued, o re kin inda, duen ar pan injar, o re kin inda: Ij me pan kak kilan?
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
Irail kin madamadaua duen me jued. Kitail kapwaiadar, karoj kileledier. Monion en aramaj me widin o meid koiok ni morjued.
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
A Kot pan kotin kajik ir edi madan, pwen kamadak on ir.
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
Pein lo arail pan kapup ir edi, o karoj, me pan kilan, pan kaurureki.
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
O aramaj karoj pan majak o inda: Mepukat Kot kotin wiadar. O re pan aja, me i japwilim a dodok.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
Me pun o pan perenki Ieowa, o pan liki i, o me lelapok kan karoj pan pereperen.

< Zabura 64 >