< Zabura 64 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
برای سالار مغنیان. مزمور داود ای خدا وقتی که تضرع می‌نمایم، آوازمرا بشنو و حیاتم را از خوف دشمن نگاه دار!۱
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
مرا از مشاورت شریران پنهان کن و ازهنگامه گناهکاران.۲
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
که زبان خود را مثل شمشیرتیز کرده‌اند و تیرهای خود یعنی سخنان تلخ را برزه آراسته‌اند.۳
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
تا در کمینهای خود بر مرد کامل بیندازند. ناگهان بر او می‌اندازند و نمی ترسند.۴
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
خویشتن را برای کار زشت تقویت می‌دهند. درباره پنهان کردن دامها گفتگو می‌کنند. می‌گویند: «کیست که ما را ببیند؟»۵
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
کارهای بد راتدبیر می‌کنند و می‌گویند: «تدبیر نیکو کرده‌ایم.» و اندرون و قلب هر یک از ایشان عمیق است.۶
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
اما خدا تیرها بر ایشان خواهد انداخت. وناگهان جراحت های ایشان خواهد شد.۷
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
وزبانهای خود را برخود فرود خواهند‌آورد و هرکه ایشان را بیند فرار خواهد کرد.۸
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
و جمیع آدمیان خواهند ترسید و کار خدا را اعلام خواهند کرد و عمل او را درک خواهند نمود.۹
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
ومرد صالح در خداوند شادی می‌کند و بر اوتوکل می‌دارد و جمیع راست دلان، فخر خواهندنمود.۱۰

< Zabura 64 >