< Zabura 64 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
Dāvida dziesma. Dziedātāju vadonim. Klausi, ak Dievs, manu balsi, kad es žēlojos; pasargi manu dzīvību no ienaidnieku briesmām.
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
Apslēp mani no ļaunu ļaužu padomiem, no ļaundarītāju trakošanas.
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
Tie savas mēles trin kā zobenu, un uzvelk savas bultas, savus rūgtos vārdus,
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
Šaut slepeni nenoziedzīgam; tie šauj viņam piepeši un nebīstas.
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
Tie iedrošinājās paši ļaunā padomā, tie runā, slepeni likt valgus, un saka: kas to redzēs?
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
Tie domā uz visādu blēdību, tiem gatavs ir viņu gudrais padoms, prātu un sirdi nevienam nevar izdibināt.
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
Bet Dievs ar bultu tos šaus piepeši, ka tiem gan sāpēs.
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
Caur savu pašu mēli tie taps apgāzti; ikkurš, kas uz tiem skatās, bēgs.
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
Un visi cilvēki bīsies un sacīs: to Dievs ir darījis, un sapratīs, ka tas ir Viņa darbs.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
Tas taisnais priecāsies iekš Tā Kunga, un paļausies uz Viņu, un visi sirdsskaidrie teiktin teiksies.