< Zabura 64 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
In finem. Psalmus David. [Exaudi, Deus, orationem meam cum deprecor; a timore inimici eripe animam meam.
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
Protexisti me a conventu malignantium, a multitudine operantium iniquitatem.
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
Quia exacuerunt ut gladium linguas suas; intenderunt arcum rem amaram,
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
ut sagittent in occultis immaculatum.
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
Subito sagittabunt eum, et non timebunt; firmaverunt sibi sermonem nequam. Narraverunt ut absconderent laqueos; dixerunt: Quis videbit eos?
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
Scrutati sunt iniquitates; defecerunt scrutantes scrutinio. Accedet homo ad cor altum,
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
et exaltabitur Deus. Sagittæ parvulorum factæ sunt plagæ eorum,
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
et infirmatæ sunt contra eos linguæ eorum. Conturbati sunt omnes qui videbant eos,
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
et timuit omnis homo. Et annuntiaverunt opera Dei, et facta ejus intellexerunt.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
Lætabitur justus in Domino, et sperabit in eo, et laudabuntur omnes recti corde.]

< Zabura 64 >