< Zabura 64 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
Pour la fin, psaume de David. Exaucez, ô Dieu, ma prière, lorsque je vous supplie: de la crainte d’un ennemi délivrez mon âme.
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
Vous m’avez protégé contre l’assemblée des méchants, et contre la multitude de ceux qui opèrent l’iniquité.
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
Parce qu’ils ont aiguisé leurs langues comme un glaive: ils ont tendu leur arc, chose amère,
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
Afin de lancer des flèches dans les ténèbres, contre un innocent.
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
Ils les lanceront soudainement contre lui, et ils ne craindront point: ils se sont affermis dans un discours pervers.
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
Ils ont cherché avec soin des iniquités contre moi; ceux qui les cherchaient ont défailli dans ces recherches.
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
Mais Dieu sera exalté. Les plaies qu’ils ont faites sont devenues des flèches de petits enfants.
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
Et leurs langues ont perdu leur force, en se tournant contre eux-mêmes. Tous ceux qui les voyaient ont été troublés,
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
Et tout homme a été saisi de crainte. Et ils ont annoncé les œuvres de Dieu, et ils ont compris les choses qu’il a faites.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
Le juste se réjouira dans le Seigneur, et il espérera en lui, et tous les hommes droits de cœur seront loués.

< Zabura 64 >