< Zabura 64 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
Au maître-chantre. — Psaume de David. Dieu, écoute ma voix, quand je gémis; Protège ma vie contre l'ennemi qui m'épouvante!
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
Mets-moi à l'abri des complots des méchants, De la foule bruyante des ouvriers d'iniquité.
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
Ils aiguisent leur langue comme une épée; Ils ajustent comme une flèche leur parole amère,
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
Pour tirer en cachette sur l'innocent. Ils tirent sur lui à l'improviste: aucune crainte ne les retient.
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
Ils s'affermissent dans leur mauvais dessein; Ils ne parlent que de tendre des pièges. Ils disent: «Qui nous verra?»
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
Ils ne songent qu'à commettre des crimes: «Nous voilà prêts, disent-ils; l'embûche est bien dressée!» Oui, les pensées secrètes, le coeur de l'homme, sont un abîme.
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
Mais Dieu leur lance un trait; Soudain les voilà frappés!
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
Ils chancellent; leur calomnie retombe sur eux. Tous ceux qui les voient hochent la tête.
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
Les hommes sont tous saisis de crainte; Ils racontent l'oeuvre de Dieu, Et ils comprennent ce qu'il a fait.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
Le juste se réjouira en l'Éternel, Et il cherchera son refuge en lui. Tous ceux qui ont le coeur droit seront pleins d'allégresse.

< Zabura 64 >