< Zabura 64 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
Psaume de David, [donné] au maître chantre. Ô Dieu! écoute ma voix quand je m'écrie; garde ma vie de la frayeur de l'ennemi.
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
Tiens-moi caché loin du secret conseil des malins, [et] de l'assemblée tumultueuse des ouvriers d'iniquité;
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
Qui ont aiguisé leur langue comme une épée; et qui ont tiré pour leur flèche une parole amère.
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
Afin de tirer contre celui qui est juste jusque dans le lieu où il se croyait en sûreté; ils tirent promptement contre lui; et ils n'ont point de crainte.
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
Ils s'assurent sur de mauvaises affaires, [et] tiennent des discours pour cacher des filets; [et] ils disent: Qui les verra?
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
Ils cherchent curieusement des méchancetés; ils ont sondé tout ce qui se peut sonder, même ce qui peut être au-dedans de l'homme, et au cœur le plus profond.
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
Mais Dieu a subitement tiré son trait contr’eux, et ils en ont été blessés.
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
Et ils ont fait tomber sur eux-mêmes leur propre langue; ils iront çà et là; chacun les verra.
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
Et tous les hommes craindront, et ils raconteront l'œuvre de Dieu, et considéreront ce qu'il aura fait.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
Le juste se réjouira en l'Eternel, et se retirera vers lui; et tous ceux qui sont droits de cœur s'en glorifieront.

< Zabura 64 >