< Zabura 64 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
God, listen to me as I tell you the things that I am worried about. I am afraid of my enemies; so save/rescue me from them.
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
Protect me from what wicked men are planning to do to me; protect me from that gang of men who do what is evil.
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
The hostile things they say [MTY] are like [SIM] [sharp] swords; their cruel words are like [SIM] arrows.
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
Without being afraid, they [lie about people and slander people] who have not done what is wrong, like someone who suddenly jumps up from where he is hiding and shoots [arrows] at his enemy [MET].
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
They encourage each other about doing the evil things that they are planning to do; they talk [with each other] about where they can set traps to catch people, and they think, “No one [RHQ] will see what we are doing,
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
because we have planned very well the crime that we are going to commit!” No one can fully understand what people can think and plan!
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
But [it will be as though] God will shoot his arrows at them, and suddenly they will be wounded.
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
Because of what they say [MTY], he will get rid of them, and then everyone who sees [what has happened to] them will shake their heads [to ridicule them].
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
And then everyone will be afraid [to sin because of what might happen to them, also]; they will tell others what God has done, and they themselves will think much about it.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
Righteous people should rejoice because of what Yahweh [has done]; they should go to him to (find protection/be safe); and all those who are godly will praise him.