< Zabura 64 >
1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
To the Chief Musician. A Melody of David. Hear, O God, my voice when I complain, From dread peril by the foe, wilt thou guard my life.
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
Wilt thou hide me, From the conclave of evil-doers, From the crowd of workers of iniquity.
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
Who have sharpened, like a sword, their tongue, Have made ready their arrow—a bitter word;
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
To shoot, in secret places, at the blameless one, Suddenly they shoot at him, and fear not.
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
They strengthen for them a wicked word, They talk of hiding snares, They have said, Who can see them?
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
They devise perverse things, They have completed the device well devised, Both the intent of each one, and the mind, are unsearchable.
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
Once let God have shot at them an arrow, Suddenly have appeared their own wounds!
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
When they were to have ruined another, their tongue smote themselves, All who observe them take flight.
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
Therefore have all men feared, —And have told the doing of God, And, his work, have considered.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
The righteous man shall rejoice in Yahweh, and seek refuge in him, Then shall glory—all who are upright in heart.