< Zabura 64 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
“For the leader of the music. A psalm of David.” Hear my voice, O God! when I pray! Preserve my life from the terrors of the enemy!
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
Hide me from the assembly of the wicked, From the brawling crowd of evil-doers!
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
For like a sword they sharpen their tongues, Like arrows they aim their poisoned words,
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
To shoot in secret at the upright; Suddenly do they shoot at him without fear.
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
They prepare themselves for an evil deed; They commune of laying secret snares: “Who,” say they, “will see them?”
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
They meditate crimes: “We have finished,” say they, “our plans!” The heart and bosom of every one of them are deep.
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
But God will shoot an arrow at them; Suddenly shall they be wounded.
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
Thus their own tongues shall bring them down; All who see them will flee away.
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
Then will all men stand in awe, And declare what God hath done, And attentively consider his work.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
The righteous shall rejoice, and trust in the LORD; All the upright in heart shall glory.

< Zabura 64 >