< Zabura 64 >

1 Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka ji ni, ya Allah, yayinda nake faɗin abin da yake damuna; ka tsare raina daga barazanan abokin gāba.
For the choirmaster. A Psalm of David. Hear, O God, my voice of complaint; preserve my life from dread of the enemy.
2 Ka ɓoye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, daga daure dauren wannan taro masu aikata mugunta.
Hide me from the scheming of the wicked, from the mob of workers of iniquity,
3 Sukan wāsa harsunansu kamar takuba su harba kalmominsu kamar kibiyoyi masu kisa.
who sharpen their tongues like swords and aim their bitter words like arrows,
4 Sukan yin kwanto su harbi marar laifi; sukan yi harbi nan da nan, ba tsoro.
ambushing the innocent in seclusion, shooting suddenly, without fear.
5 Sukan ƙarfafa juna a mugayen ƙulle-ƙullensu, sukan yi magana yadda za su ɓoye tarkunansu; su ce, “Wa zai gan su?”
They hold fast to their evil purpose; they speak of hiding their snares. “Who will see them?” they say.
6 Sukan yi ƙulle-ƙullen rashin adalci su ce, “Mun gama ƙulla cikakkiyar maƙarƙashiya tsab!” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa.
They devise injustice and say, “We have perfected a secret plan.” For the inner man and the heart are mysterious.
7 Amma Allah zai harbe su da kibiyoyi; nan da nan za a buge su su fāɗi.
But God will shoot them with arrows; suddenly they will be wounded.
8 Zai juya harshensu a kansu yă kuma kawo su ga hallaka; duk waɗanda suka gan su za su kaɗa kai, suna musu ba’a.
They will be made to stumble, their own tongues turned against them. All who see will shake their heads.
9 Dukan mutane za su ji tsoro; za su yi shelar ayyukan Allah su kuma yi tunanin abin da ya aikata.
Then all mankind will fear and proclaim the work of God; so they will ponder what He has done.
10 Bari masu adalci su yi farin ciki a cikin Ubangiji su kuma nemi mafaka a gare shi; bari dukan masu gaskiya a zuciya su yabe shi!
Let the righteous rejoice in the LORD and take refuge in Him; let all the upright in heart exult.

< Zabura 64 >