< Zabura 63 >
1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
Oh Dios, tú eres mi Dios; de madrugada te buscaré: mi alma está seca por necesidad de ti, mi carne se desperdicia con deseo por ti, como una tierra seca y ardiente donde no hay agua;
2 Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
Para ver tu poder y tu gloria, como te he visto en el lugar santo.
3 Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
Porque tu misericordia es mejor que la vida, mis labios te darán alabanza.
4 Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
Así que continuaré bendiciéndote toda mi vida, levantando mis manos en tu nombre.
5 Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
Mi alma será consolada, como con buena comida; y mi boca te dará alabanza con canciones de alegría;
6 A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
Cuando el recuerdo de ti viene a mí en mi cama, y cuando pienso en ti por la noche.
7 Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
Porque has sido mi ayuda, tendré gozo a la sombra de tus alas.
8 Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
Mi alma se mantiene siempre cerca de ti: tu diestra es mi apoyo.
9 Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
Pero aquellos cuyo deseo es la destrucción de mi alma bajará a las partes más bajas de la tierra.
10 Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
Serán cortados por la espada; serán alimento para zorros.
11 Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.
Pero el rey tendrá gozo en Dios; todos los que juran por él tendrán motivos de orgullo; pero la boca falsa se detendrá.