< Zabura 63 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
Salmo de David, estando en el desierto de Judá. DIOS, Dios mío eres tú: levantaréme á ti de mañana: mi alma tiene sed de ti, mi carne te desea, en tierra de sequedad y transida sin aguas;
2 Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
Para ver tu fortaleza y tu gloria, así como te he mirado en el santuario.
3 Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
Porque mejor es tu misericordia que la vida: mis labios te alabarán.
4 Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
Así te bendeciré en mi vida: en tu nombre alzaré mis manos.
5 Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
Como de meollo y de grosura será saciada mi alma; y con labios de júbilo te alabará mi boca,
6 A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
Cuando me acordaré de ti en mi lecho, [cuando] meditaré de ti en las velas de la noche.
7 Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
Porque has sido mi socorro; y [así] en la sombra de tus alas me regocijaré.
8 Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
Está mi alma apegada á ti: tu diestra me ha sostenido.
9 Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
Mas los que para destrucción buscaron mi alma, caerán en los sitios bajos de la tierra.
10 Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
Destruiránlos á filo de espada; serán porción de las zorras.
11 Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.
Empero el rey se alegrará en Dios; será alabado cualquiera que por él jura: porque la boca de los que hablan mentira, será cerrada.

< Zabura 63 >