< Zabura 63 >
1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
Un salmo de David, cuando estaba en el desierto de Judá. Dios, tú eres mi Dios y te busco de todo corazón. Mi ser entero te anhela y tiene sed de ti, en medio de esta tierra seca, árida y carente de aguas.
2 Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
Te veo en el Templo. Contemplo tu poder y tu gloria.
3 Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
Tu fidelidad y amor son mejores que la vida misma. Por ello te alabaré.
4 Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
Te agradeceré tanto como viva. Elevo mis manos hacia ti y celebro tu maravilloso carácter.
5 Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
Tú me satisfaces más que el mejor de los alimentos. Te alabaré con canciones alegres.
6 A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
Paso la noche entera pensando en ti desde que me acuesto, meditando sobre ti.
7 Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
Porque eres quien me ayuda, canto feliz bajo tus alas.
8 Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
Me aferro a ti y tus fuertes brazos me levantan.
9 Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
Los que tratan de destruirme irán a la tumba.
10 Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
Morirán a punta de espada y serán alimento para los chacales.
11 Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.
Pero el rey vivirá feliz por todo lo que Dios ha hecho. Todos los que siguen a Dios le alabarán, pero los que mienten serán silenciados.