< Zabura 63 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
Salmo de Davi, quando ele estava no deserto de Judá: Deus, tu [és] meu Deus. Eu te busco ao amanhecer; minha alma tem sede de ti, minha carne muito te deseja, em terra seca, cansativa, sem águas.
2 Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
Para que eu te veja em teu santuário, para ver tua força e tua glória.
3 Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
Porque tua bondade [é] melhor que a vida; meus lábios te louvarão.
4 Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
Assim te bendirei em minha vida; por teu nome levantarei minhas mãos.
5 Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
Minha alma será saciada, como que de gorduras e muita comida; e minha boca te louvará com lábios alegres,
6 A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
Quando eu me lembrar de ti em minha cama; nas vigílias da noite meus pensamentos estarão em ti.
7 Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
Porque tu tens sido meu socorro; e à sombra de tuas asas cantarei de alegria.
8 Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
Minha alma está apegada a ti; tua mão direita me sustenta.
9 Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
Porém aqueles que procuram assolar a minha alma irão para as profundezas da terra.
10 Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
Eles serão derrubados pela força da espada; serão repartidos entre raposas.
11 Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.
Mas o Rei se alegrará em Deus; todo o que por ele jurar se alegrará, porque a boca dos mentirosos será tapada.

< Zabura 63 >