< Zabura 63 >
1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
Ó Deus, tu és o meu Deus, de madrugada te buscarei: a minha alma tem sede de ti; a minha carne te deseja muito em uma terra seca e cançada, onde não há água
2 Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
Para ver a tua fortaleza e a tua glória, como te vi no santuário.
3 Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
Porque a tua benignidade é melhor do que a vida; os meus lábios te louvarão.
4 Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
Assim eu te bendirei enquanto viver: em teu nome levantarei as minhas mãos.
5 Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
A minha alma se fartará, como de tutano e de gordura; e a minha boca te louvará com alegres lábios,
6 A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
Quando me lembrar de ti na minha cama, e meditar em ti nas vigílias da noite.
7 Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
Porque tu tens sido o meu auxílio; portanto na sombra das tuas asas me regozijarei.
8 Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
A minha alma te segue de perto: a tua dextra me sustenta.
9 Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
Mas aqueles que procuram a minha alma para a destruir, irão para as profundezas da terra.
10 Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
Cairão à espada, serão uma ração para as raposas.
11 Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.
Mas o rei se regozijará em Deus; qualquer que por ele jurar se glóriará; porque se taparão as bocas dos que falam a mentira.