< Zabura 63 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
Ein Psalm Davids, als er in der Wüste Juda war. Gott, du bist mein Gott, dich suche ich! Es dürstet nach dir meine Seele, es schmachtet nach dir mein Leib, in dürrem, lechzendem Land ohne Wasser.
2 Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
So hab' ich dich im Heiligtume geschaut, um deine Macht und Herrlichkeit zu sehen.
3 Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
Denn deine Gnade ist besser als Leben; meine Lippen sollen dich loben.
4 Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
Also will ich dich preisen mein Leben lang, in deinem Namen meine Hände erheben.
5 Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
Wie an Mark und Fett ersättigt sich meine Seele, und mit Jubellippen rühmt mein Mund,
6 A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
wenn ich auf meinem Lager deiner gedenke, in den Nachtwachen über dich sinne.
7 Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
Denn du warst meine Hilfe und im Schatten deiner Flügel juble ich.
8 Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
Getreulich hängt dir meine Seele an; aufrecht hält mich deine Rechte.
9 Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
Jene aber - zu ihrem Verderben trachten sie mir nach dem Leben; in die Tiefen der Erde werden sie hinabfahren.
10 Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
Man wird ihn dem Schwerte preisgeben; der Schakale Beute werden sie.
11 Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.
Aber der König wird sich Gottes freuen; rühmen wird sich jeder, der bei ihm schwört, daß den Lügenrednern der Mund gestopft ward.

< Zabura 63 >