< Zabura 63 >
1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
O Dieu, tu es mon Dieu, je te cherche au point du jour; mon âme a soif de toi, ma chair te souhaite, dans cette terre aride, desséchée, sans eau,
2 Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
Pour voir ta force et ta gloire, comme je t'ai contemplé dans le sanctuaire.
3 Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
Car ta bonté est meilleure que la vie; mes lèvres chanteront ta louange.
4 Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
Ainsi je te bénirai pendant ma vie; j'élèverai mes mains en ton nom.
5 Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
Mon âme est rassasiée comme de mœlle et de graisse; ma bouche te loue avec des cris de réjouissance;
6 A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
Quand je me souviens de toi sur mon lit, et que je médite sur toi pendant les veilles de la nuit.
7 Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
Car tu as été mon secours; aussi je me réjouirai sous l'ombre de tes ailes.
8 Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
Mon âme s'est attachée à toi pour te suivre, et ta droite me soutient.
9 Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
Mais ceux qui cherchent ma vie pour la détruire, descendront dans les profondeurs de la terre.
10 Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
Ils seront livrés au tranchant de l'épée; ils seront la proie des renards.
11 Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.
Mais le roi se réjouira en Dieu, et quiconque jure par lui, s'en glorifiera; car la bouche de ceux qui parlent faussement sera fermée.