< Zabura 63 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
Psaume de David, lorsqu'il était dans le désert de Juda. Ô Dieu! tu es mon [Dieu] Fort, je te cherche au point du jour; mon âme a soif de toi, ma chair te souhaite en cette terre déserte, altérée, [et] sans eau.
2 Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
Pour voir ta force et ta gloire, ainsi que je t'ai contemplé dans ton Sanctuaire.
3 Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
Car ta gratuité est meilleure que la vie; mes lèvres te loueront.
4 Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
Et ainsi je te bénirai durant ma vie, [et] j'élèverai mes mains en ton Nom.
5 Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
Mon âme est rassasiée comme de mœlle et de graisse; et ma bouche te loue avec un chant de réjouissance.
6 A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
Quand je me souviens de toi dans mon lit, je médite de toi durant les veilles de la nuit.
7 Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
Parce que tu m'as été en secours, à cause de cela je me réjouirai à l'ombre de tes ailes.
8 Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
Mon âme s'est attachée à toi pour te suivre, [et] ta droite me soutient.
9 Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
Mais ceux-ci qui demandent que mon âme tombe en ruine, entreront au plus bas de la terre.
10 Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
On les détruira à coups d'épée; ils seront la portion des renards.
11 Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.
Mais le Roi se réjouira en Dieu; [et] quiconque jure par lui s'en glorifiera; car la bouche de ceux qui mentent sera fermée.

< Zabura 63 >