< Zabura 63 >

1 Zabura ta Dawuda. Sa’ad da yake a hamadar Yahuda. Ya Allah, kai ne Allahna, da nacewa na neme ka; raina yana ƙishinka, jikina yana marmarinka, cikin busasshiyar ƙasar da ta zozaye inda babu ruwa.
God, you are the God whom I [worship]. I greatly desire to be with you like [SIL] a person in a dry hot desert greatly desires [some cool water].
2 Na gan ka a wuri mai tsarki na kuma dubi ikonka da ɗaukakarka.
So, I want to see you in your temple; I want to see that you are great and glorious.
3 Domin ƙaunarka ta fi rai kyau, leɓunana za su ɗaukaka ka.
Your constantly loving [me] is (worth more/more precious) than [my] life, so I [MTY] will [always] praise you.
4 Zan yabe ka muddin raina, kuma a cikin sunanka zai ɗaga hannuwana.
I will praise you all the time that I live; I will lift up my hands to you while I pray.
5 Raina zai ƙoshi kamar da abinci mafi kyau; da leɓunan rerawa bakina zai yabe ka.
[Knowing you satisfies me more than] [IDM, MET] my eating a very big feast, [so] I will praise you while I sing [MTY] joyful songs.
6 A gadona na tuna da kai; ina tunaninka dukan dare.
While I lie on my bed, I think about you. I think/meditate about you all during the night,
7 Domin kai ne mai taimakona, ina rera a cikin inuwar fikafikanka.
because you have always helped me, and I sing joyfully knowing that I am protected by you [as a little bird is protected] under [its mother’s] wings [MET].
8 Raina ya manne maka; hannunka na dama yana riƙe da ni.
I cling to you; and with your hand/power you protect me.
9 Su da suke neman raina za su hallaka; za su gangara zuwa zurfafan duniya.
But those who are trying to kill me will [die and] descend into the place of the dead;
10 Za a bayar da su ga takobi su kuma zama abincin karnukan jeji.
they will be killed in battles [MTY] and their [corpses] will be eaten by jackals/wild dogs.
11 Amma sarki zai yi farin ciki ga Allah; dukan waɗanda suke rantse da sunan Allah za su yabe shi, amma za a rufe bakunan maƙaryata.
But I, the king [of Israel], will rejoice in what God has done; and all those who revere and trust God will praise him, but he will not allow liars to say anything.

< Zabura 63 >